Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 07/10/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 07/10/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Habiba Adamu da Aisha Babangida

  1. Wakilan Hamas na buƙatar tabbaci daga Trump kan kawo ƙarhen yaƙin Gaza

    Trump

    Asalin hoton, EPA

    Yayin da aka shiga kwana na biyu a tattaunawar da ba ta keke da keke ba tsakanin wakilan Isra'ila da Hamas, babban wakilin kungiyar Khalil al-Hayya ya ce Hamas na bukatar tabbaci daga shugaba Trump kan duk wata tattauna ko yarjejeniyar da za a cimma za ta tabbatar da an kawo karshen yakin da ake yi Gaza baki daya.

    Sai dai wakiliyar BBC ta ce Isra'ila na son maida hankali ne kan matakin farko na yarjejeniyar wato sako wadanda akai garkuwa da su, da bayanin inda za a sake su da wadanda za su jagoranci hakan.

    Yayin da wakilan bangarorin biyu ke can Masar tattauna kawo karshen yakin, can a zirin Gaza tankokin yaki da makaman rokar Isra'ila na ci gaba da barin wuta kan Falasdinawa.

  2. Gwamnatin Burkina Faso ta kama wasu turawa kan zargin leƙen asiri

    Shugaban Burkina Faso

    Asalin hoton, Reuters

    Gwamnatin mulkin sojin Burkina Faso ta ce ta kama wasu mutum takwas mambobin wata ƙungiyar agaji ta ƙasar Netherland.

    Mutanen sun kunshi wasu ƴankasashen Turai uku da ɗan Mali huɗu ɗaya da kuma ƴan Burkina Faso huɗu.

    Ana zargin duka mutanen takwas - ƴan ƙungiyar INSO - da laifin leƙen asiri.

    Sojojin Burkina Faso, da suka ƙwace mulki a juyin mulki shekara uku da suka gabata na takun saƙa da ƙungiyoyin agajin ƙasashen Turai.

  3. Manomin Afirka ta Kudu ya musanta ciyar da aladunsa ƴan mata baƙaƙen fata

    Manomin nan farar fata da ake zargi da kashe wasu mata biyu bakar fata a arewacin lardin Limpopo na Afirka ta Kudu a bara, ya musanta aikata kisan a shari'ar da ta janyo tashin hankali a kasar.

    Ana tuhumar Johannes Olivier da laifin kashe matan biyu a gonarsa da ke kusa da Polokwane, inda ya ciyar da aladunsa naman mamatan.

    Maria Makgato da Kudzai Ndlovu, sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da suka je neman madarar da ta kusan lalacewa da aka bari domin aladun su sha.

    Olivier mai shekara 61, ya kare matakin harbin da ya yi da cewa na gargadi ne amma da ya duba sai ya ga sun mutu, don haka ya jefa su cikin dakin aladun.

    Sai washegari sannan ya kira 'yansanda ta waya tare da shaida musu ya jefar da bindigar da ya yi harbin da ita.

  4. Ministan kimiyya da fasaha na Najeriya ya yi murabus kan zargin digirin bogi

    Nnaji

    Asalin hoton, Bayo Onanuga

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da murabus ɗin ministan kimiyya da fasaha na Najeriya Geoffrey Uche Nnaji.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Najeriya Bayo Onanuga ya fitar, ya ce shugaban ya amince da murabus ɗin ministan, wanda ya biyo bayan zarginsa da aka yi da amfani da digirin bogi.

    An dai zargi tsohon minista ne da amfani da digirin bogi daga Jami'ar Najeriya ta Nsuka, lamarin da ya ja hankalin ƴan ƙasar matuƙa, duk da ya musanta.

    Njaji ya ce ana masa bita da ƙulli ne, lamarin da ya zargi "abokan hamayyarsa a siyasa" da yunƙurin ɓata masa suna.

    Tinubu ya yi godiya a gare shi "bisa hidimta wa Najariya" sannan ya yi masa fatan alheri.

  5. Masu shiga tsakani na Isra'ila da Hamas na ci gaba da tattaunawa a Masar

    Masu shiga tsakani daga Isa'ila da Hamas sun shafe tsawo sa'o'i huɗu suna tattaunawar da ba ta keke da ƙeƙe ba kan yadda za a kawo ƙarshen yakin Gaza.

    Wata majiyar Falasɗinu mai masaniya game da tattaunawa da ake yi a birnin Sharm el-Sheikh ta shaida wa BBC cewa an amince da ƙudurori biyar a daftarin yarjejeniyar.

    Wani babban jami'in Hamas ya ce wakilan na ƙoƙarin amincewa da abin da zai daɗaɗa wa mutanen Gaza.

    Ma'aikatar harkokin wajen Qatar - wadda ke zaman ɗaya daga cikin masu shiga tsakanin - ta ce akwai abubuwa masu yawa da za a tattauna a kansu cikin ƙudurori 20 da Trump ya gabatar a daftarin yarjejeniyar.

    Tankokin Isra'ila da jiragen yaƙinta sun ci gaba da kai hare-hare a wasu yankunan Gaza a yau.

    Ana sa ran wakilin Amurka na musamman, Steve Witkoff da mai bai wa shugaban ƙasa shawara Jared Kushner za su halarci tattaunawar a ranar Laraba.

  6. Tinubu ya karrama tsohon shugaban INEC da lambar CON kan 'hidimta wa Najeriya'

    INEC

    Asalin hoton, Bayo Onanuga

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da sauka daga shugabancin hukumar zaɓe ta Najeriya, INEC da Farfesa Mahmood Yakubu ya yi bayan kammala wa'adinsa na biyu a ofis.

    An naɗa Yakubu a matsayin shugaban hukumar ne a ranar 14 ga watan Nuwamban 2015, inda ya yi wa'adi biyu na shekara biyar-biyar.

    An sabunta masa wa'adin ne a shekarar 2020, wa'adin da a yanzu ya ƙare bayan shekara biyar, wanda ya kama shekara 10 jimilla yana shugabantar hukumar.

    Tinubu ya yaba a ƙoƙarinsa wajen "hidimta wa Najeriya da kuma ƙoƙarin da ya yi wajen inganta dimokuraɗyyar Najeriya musamman ta hanyar shirya zaɓe ingantacce a wa'adinsa biyu a hukumar INEC," in ji Tinubu a sanarwar da mai magana da yawunsa, Bayo Onaguga ya fitar.

    Tinubu ya kuma karrama tsohon shugaban hukumar da lambar yabo ta CON domin "jinjina wa ƙoƙarinsa wajen aiki."

    Tuni dai Tinubu ya umarci Yakubu ya miƙa shugabancin hukumar ga babbar kwamishinar hukumar May Agbamuche-Mbu, wadda za ta yi riƙon-ƙwarya kafin a naɗa sabon shugaba na dindindin.

  7. Wutar solar ta zama lantarkin da aka fi amfani da ita a duniya - Rahoto

    Panel na sola

    Asalin hoton, Getty Images

    Wutar solar ko lantarki mai amfani da hasken rana da iska sun zarce wutar da ake samu daga makamashin kwal karon farko cikin tarihi a duniya, cewar sabbin alƙaluma daga cibiyar Ember mai nazarin makamashi.

    Wutar solar na samar da ƙarin lantarkin da ake nema da kashi 100, kuma hakan ya taimaka wajen rage amfani da makamashin kwal da iskar gas a matsayin hanyar samun lantarki.

    Afirka ta Kudu mai ƙarfin arziƙin makamashin kwal ita ce ke kan gaba wajen amfani da wutar solar a Afirka.

    Cibiyar ta Ember ta ce Najeriya ce a matsayi na biyu wajen amfani da ssolar a Afirka sai Masar a matsayi na uku.

    Rahoton ya ce adadin wutar sola da Najeriya ke samar wa ta kai gigawatt 1.7, wanda zai iya haskaka gidaje miliyan 1.8 a nahiyar Turai.

  8. An kama Ba'amurke da laifin safarar ma'aidai a Ghana

    Wasu jami'ai

    Asalin hoton, MINISTRY OF LANDS AND NATURAL RESOURCES/FACEBOOK

    Hukumomin Ghana sun kama wasu mutum shida, ciki har da wani Ba'amurke da wani ɗan Moroko da laifin cinikin ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba a ƙasar.

    An tsare waɗanda ake zargin a lokacin da suke yunƙurin sayen kilogiram 2.1 na zinare da aka ƙiyasta kudinsa ya kai dala 176,109.

    Jami'ai sun ce An ƙwace kayan aikin tace zinaren daga hannun Ba'amurke a lokacin samamen.

    Samamen na cikin wani yunƙuri da hukumomin Ghana ke yi na kakka be matsalar akar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba a ƙasar da aka fi sani da galamsey.

    Matsalar galamsey na haifar da mummunan illa tare da llata koguna da gonakin ƙasar.

    A baya-bayan nan gwamnatin kasar ta ƙarfafa samamen soji da nufin kawo karshen matsalar a faɗin ƙasar.

  9. Shugaban INEC ya sauka daga muƙaminsa bayan ƙarewar wa'adinsa

    Tsohon shugaban INEC

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban hukumar zaɓen Najeriya, Farfesa Mahmood Yakubu ya sauka daga muƙaminsa tare da miƙa ragamar jagorancin hukumar ga May Agbamuche wadda za ta riƙe muƙamin a matsayin riko kafin naɗa sabon shugaba.

    Farfesa Yakubu ya bayyana hakan ne ranar Talata a lokacin ganawarsa da kwamishinonin hukumar a shalkwatar zaɓen da ke Abuja.

    Agbamuche ita ce wadda ta fi kowa jimawa a matsayin babbar kwamishina a hukumar zaɓen ƙasar.

    Ya kuma yi kira da sauran kwamishinoni da daraktocin hukumar su bai wa Agbamuche cikakken goyon bayan kafin lokacin naɗa sabon shugaban hukumar.

    A watan Oktoba 2015 ne tsohon Shugaban Najeriya Marigayi, Muhammadu Buhari ya naɗa Farfesa Yakubu a matsayin shugaban hukumar INEC, wanda ya maye gurbin Farfesa Attahiru Jega.

    Haka a 2020 Muhammadu Buhari ya sake naɗa shi a karo na biyu don jagorantar hukumar a wa'adi na biyu.

    Farfesa Yakubu ya jagoranci hukumar na tsawon shekara 10, tare da gudanar da manyan zabukan kasar biyu na 2019 da 2015.

  10. Rajoelina ya naɗa janar ɗin soji don kwantar da boren matasan Madagascar

    Sabon firaministan Madagascar

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Madagascar, Andry Rajoelina ya naɗa janar ɗin soji a matsayin sabon firaiminista, a wani yunƙuri na kawo ƙarshen boren da matasa ke yi wa gwamnatinsa.

    Ya ce ƙasar na buƙatar mutumin da zai maido da doka da oda kuma wanda mutane za su aminta da shi, kafin naɗa Ruphin Fortunat Zafisambo, a matsayin wanda zai riƙe muƙamin.

    Hakan na zuwa ne bayan shugaba Rajoelina ya bayyana fargabar yunƙurin juyin mulki, kuma naɗin janar ɗin na nuni da sanya soji cikin harkar gwamnati, wadda kuma wata hanya ce ta neman goyon bayan sojoji, yayin da ake samun ƙaruwar zaman ɗar-ɗar.

    Sai dai matasan masu boren da ake yiwa laƙabi da 'Gen Z Mada,' sun yi watsi da naɗin janar Zafisambo, inda suka bai wa Rajoelina sa'oi 48 ya yi murabus.

    A ranar 25 ga watan Satumba ne matasan suka fara zanga-zangar sakamakon fusatar da al'umma suka yi saboda yanke wuta da ruwa da aka sha yi, lamarin da ya faɗaɗa zuwa nuna rashin jin daɗinsu kan batutuwan cin hanci da rashawa da rashin aikin yi da kuma tsadar rayuwa.

  11. Kotu ta dakatar da ƴansanda tilasta neman izinin sanya gilashin mota mai duhu

    .....

    Asalin hoton, Nigeria Police

    Wata kotun tarayya da ke zamanta a Warri da ke jihar Delta, ta bayar da umarnin wucin gadi na hana sfeton ƴansandan Najeriya tilasta neman izini ga masu motocin da ke sanya gilashinsu ya yi duhu.

    Umarnin ya kuma hana jami'an ƴansanda aiwatar da dokar da rundunar ta sanar wadda ta ce zai fara aiki daga ranar Litinin 6 ga watan Oktoba, 2025.

    A yayin da yake bayyana hukuncin kotun, mai shari'a Hyeladzira Nganjiwa ya amince da buƙatun mai shigar da ƙarar na hana waɗanda ake ƙarar da suka haɗa da ƴankwangila ko diloli da shugaban ƴan sanda da jami'anta yin komai a kan dokar har sai an kammala shari'ar da ke gaban kotun.

    Haka zalika umarnin ya hana ƴansanda tsayar da wasu, ko cin zarafinsu ko tsare su ko motocinsu a ƙarƙashin dokar.

    An ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 16 ga watan Oktoba, domin ci gaba da sauraron ƙarar.

  12. Amfani da makamashin da ake sabuntawa ya zarta na kwal a duniya

    ,,,,

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Makamashin da ake sabuntawa ya zarta makamashin kwal wurin samar da wutar lantarki a rabin wannan shekarar.

    Hakan shi ne karo na farko a tarihi, a cewar wasu sabbin alƙaluman kwamitin kwararru kan makamashi na duniya mai suna Ember.

    Ɓuƙatar wutar lantarki na ƙaruwa a faɗin duniya, amma an fi samun ci gaba wurin amfani da hasken rana da kuma iska wajen samar da wutar, inda hakan ya kai ga cimma kashi 100 cikin ɗari na buƙatar.

    kwamitin ya ƙara da cewa lamarin ya kuma janyo raguwar amfani da makamashin kwal da iskar gas wurin samar da lantarkin.

    Sai dai Ember ya ce ana samun bambance-bambance a ɓangarorin duniya.

    A ƙasashe masu tasowa, musamman a China, ƙasar ce a gaba wajen amfani da makamashi mai tsafta, amma a ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziki kamar Amurka da kuma nahiyar Turai sun fi dogara kan makamashin da ke ɗumama yanayi fiye da a baya don samar da wutar lantarki.

  13. Sanata Natasha ta halarci zaman majalisar Najeriya

    ..

    Asalin hoton, Others

    A karon farko, sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ta halarci zaman zauren majalisar dattawan Najeriya, bayan dakatar da ita da aka yi na watanni shida.

    A ranar Talata ne majalisar ta koma bakin aiki, bayan tsawaita lokacin komarsu da ƴan makonni.

    Sai dai sanatar mai wakiltar kogi ta arewa ta halarci zaman majalisar ne wanda shugaban Majalisar, kuma abokin rikicin Natasha, Godswill Akpabio ya jagoranta.

    Dakatar da ita ya janyo cece-kuce sosai a siyasar ƙasar, musamman saboda zargin cin zarafin da ta yi wa shugaban Majalisar Akpabio.

  14. Paul Biya zai je kamfe arewacin Kamaru

    ,,,

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Shugaban mai shekara 92 a duniya, Paul Biya zai yi yaƙin neman zaɓe a yankin arewa mai nisa a Kamaru, yankin da ke da yawan ƙuri'u a ranar Talata, gabannin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

    Wannan ne karo na farko da shugaban zai bayyana a bainar jama'a tun bayan fara kamfe fiye da mako guda.

    Biya zai ziyarci birnin Maroua, inda ya yi yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar a 2018.

    An jima ba a ga shugaba Paul Biya ba a sha'anin siyasar ƙasar, domin ya fi dogaro sosai da ministocinsa da ke yi masa yaƙin neman zaɓe a ƙasar.

    Yayin da abokan adawar takarar shugabancin ƙasar ke shirin shiga guguwar yaƙin neman zaɓen, shi kuma Paul Biya ya taho ne daga Turai domin yin kwana 10 a ƙasar.

    Duk da kiraye-kirayen da ake masa na ya sauka, Shugaba Biya ya shaida wa mutanen ƙasar cewa har yanzu yana da sauran abun da zai yi musu bayan shafe kusan shekara 43 a kan mulki.

  15. An nemi Macron ya gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da wuri

    ,,,,

    Asalin hoton, EPA/Shutterstock

    Tsohon firaiministan Faransa ya buƙaci shugaba, Emmanuel Macron, da ya bayyana sabon firaiminista, ya amince da kasafin kuɗin ƙasar kuma ya ayyana yin babban zaɓe da wuri, don magance rikita-rikitar siyasar da ƙasar ke fuskanta.

    Édouard Philippe wanda shi ne firaiminista na farko a gwamnatin Macron ya bayyana hakan ne bayan firaiminista na uku a cikin shekara ɗaya, Sébastien Lecornu ya yi murabus a ranar Litinin.

    Lecornu ya sauka daga muƙaminsa ne bayan yunƙurin kafa gwamnatin da bai yi nasara ba.

    Philippe, wanda ya yi firaiminista daga shekarar 2017 zuwa 2020, yanzu yana jagorantar jam'iyyar Horizons mai matsakaicin ra'ayi, kuma ya ce baya goyon bayan wanda ya gaje shi bare kuma murabus ɗinsa na ba zata, sai dai ya rage ga shugaban ƙasar ya yi abun da aka zaɓe shi don yi.

    Kafin yanzu dai matsin lamba kan shugaba Macron mai shekara 47 na ya sauka daga muƙaminsa, ya fi ƙarfi ta ɓangaren abokan adawarsa masu ra'ayin riƙau da masu ra'ayin sassauci.

    Sai dai fitowa bainar jama'a da abokan tafiyarsa ke yi suna kare shi, a yanzu na nuni da ƙamarin da matsalar siyasar ke yi.

  16. Satar wayar iphone ta bankaɗo gungun masu safarar waya a London

    ,,,

    Ƴansanda a London sun ce sun tarwatsa wata ƙungiyar barayi ta ƙasa da ƙasa da ta kwace tare da safarar wayoyin salular jama'a kimanin 40,000 zuwa China.

    Magajin garin birnin, Sadiq Khan, ya ce ƴansanda sun dirar wa shugabannin masu aikata laifukan ciki har da masu ƙwacen waya a kan tituna.

    Aƙalla mutane 16 aka kama, a binciken da aka kwashe shekara guda ana yi.

    Wakiliyar BBC ta ce tuni aka gurfanar da mutum uku, ciki har da ƴan Afghanistan da ake zargi da hannu a lamarin.

    Ana tunanin suna sayar da kowacce waya guda ɗaya a kan kusan dalar Amurka 5000 saboda a buɗe suke, saɓanin wayoyin da ake sayarwa a China.

  17. An buƙaci kotu ta hana Jonathan tsayawa takara

    ,,,,

    Asalin hoton, Independent Newspaper

    An nemi wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, ta dakatar da tsohon shugaba ƙasa, Goodluck Jonathan daga tsayawa takarar shugabancin Najeriya a zaɓen 2027 ko kowane zaɓen shugaban ƙasar da za a yi nan gaba.

    An miƙa buƙatar hakan ne a cikin wata ƙara da wani lauya, Johnmary Jideobi ya shigar gaban kotun.

    Buƙatar ta kuma nemi a hana hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC karɓa ko wallafa sunan tsohon shugaban ƙasar, a matsayin ɗantakara tare da neman ofishin babban mai gabatar da ƙara na ƙasar ya bi wannan umarnin.

    Mai ƙarar ya bayyana cewa Jonathan ya ƙarasa wa'adin mulkin marigayi shugaba Umaru Musa Ƴar Aduwa, sannan ya yi sabon wa'adi na shekara huɗu bayan cin zaɓen 2011, don haka ya kammala wa'adi biyu da kundin tsarin mulki ya tanadar.

    Sai dai ba a sanya ranar fara sauraron ƙarar ba.

  18. Majalisa na yunƙurin ganin an sanya ido kan kirifto a Najeriya

    ,,,,

    Asalin hoton, Reuters

    Majalisar wakilan Najeriya ta fara yunƙurin ganin an ɗauki matakan sanya ido kan harkokin da suka shafi hada-hadar kuɗaɗe na intanet na kirifto da na'urar POS.

    A ranar Litinin ne kakakin majalisar, Abbas Tajudeen ya ƙaddamar da wani kwamiti wanda zai duba amfani ta ɓangaren tattalin arziki da yadda za a sanya ido kan su da kuma tsaron hada-hadar da akeyi ta hanyar intanet.

    A jawabin da ya gabatar kakakin majalisar ya ce matakin ya zama dole, idan aka yi la'akari da damuwar da ake nunawa kan damfara da manyan laifukan intanet da samar da kuɗaɗen don aikata ta'addanci da ayyukan masu kirifto da na POS da ke cutar da masu mu'amala da su.

    Inda ya ƙara da cewa rashin dokoki na zahiri da sauye-sauye da sarƙaƙiyar da ke tattare da fasaha, suka sa dole majalisar ta kafa wasu dokoki na sa ido da kula, da kuma bayar da kariya ga masu amfani da kirifto da kuma POS a ƙasar.

    Ana sa ran kwamitin zai yi zaman jin bahasi don tattara bayanai daga masu ruwa da tsaki domin taimaka wa majalisar wajen yin dokar da zata tsara yadda za a tafiyar da ayyukan kirifto da sauran ayyukan hada-hadar kuɗaɗe na intanet a ƙasar.

  19. Trump zai yi amfani da ƙarfin tsarin mulki don kai dakaru biranen Amurka

    ,,,

    Asalin hoton, EPA

    Shugaba Donald Trump ya ce yana tunanin yin amfani da wani ƙarfi na musamman da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba wa shugaban kasa, wajen daƙile adawar da ake nunawa wa shirinsa na amfani da jami'an tsaro wurin don tsaftace biranen ƙasar daga masu aikata laifuka.

    Dokar ta ba wa shugaban ƙasa wata dama ta musamman ta tura sojoji kowanne yanki na ƙasar ba tare da wani shamaki ba, wani iko da ba safai shugabannin ƙasar suka fiye amfani da shi ba.

    Ko da yake Mista Trump ya ce ba ya buƙatar yin hakan a yanzu, to amma fa idan tura ta kai bango, wato gwamnonin Democrat da alƙalai suka ci gaba adawa da shirin na sa, to babu makawa zai yi amfani da damar da yake da ita.

    Gargaɗin nasa na zuwa ne kwana guda bayan wani alƙali ya yanke hukuncin hana tura dakarun zuwa birnin Portland a jihar Oregon.

    Gwamnonin Democrat dai na zargin Trump da amfani da jami'an na tarayya a matsayin wani makamin siyasa.