Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 04/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 4 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • An ɗage taron jana'izar Khamenei
  • Ana zargin mutum 140 sun ɓace bayan nutsewar jirgin ruwan Iran a gabar Sri Lanka
  • 'An yi yunƙurin kai hari da jirgi mara matuƙi kan babban matatar man Saudiyya'
  • Ghana ta rufe ofishin jakadancinta a Tehran saboda rikicin Gabas ta Tsakiya
  • Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka a Qatar
  • Amurka ta yi iƙirarin kai hare-hare kusan wurare 2000 a Iran tun bayan fara yaƙi
  • Ministan harkokin wajen Iran ya zargi Trump da wargaza tattaunawar sulhu da gangan
  • Iran ta tabbatar da kisan Ali Khamenei a hare-haren Amurka da Isra'ila

Rahoto kai-tsaye

Daga AIsha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Me ya sa Amurka da Isra'ila suka kai wa Iran hari, kuma yaushe yaƙin zai ƙare?

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rikici ya ɓarke a Gabas ta Tsakiya bayan kashe jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei, a wasu hare-haren da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar.

    Bayan harin, shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci al'ummar Iran su tuntsurar da gwamnati.

    A matsayin martani, Iran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa a wurare da dama na yankin, kamar ƙasashen Isra'ila da Bahrain da Kuwait da Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa da Jordan da Saudiyya da tsibirin Cyprus, har ma da jiragen dakon man fetur da ke ratsawa ta mashigar Hormuz.

    Haka nan ma ƙungiyar Hezbollah mai samun goyon bayan Iran da ke a Lebanon ta shiga faɗan, inda ta harba rokoki zuwa cikin Isra'ila daga sansanoninta da ke cikin Lebanon.

    Isra'ila ta mayar da martani ta hanyar kai hari kan cibiyoyin Hezbollah a Lebanon.

  2. Yadda kisan Ali Khamenei zai shafi ƴan Shi'a a Najeriya

    ....

    Asalin hoton, JNIM

    Har yanzu duniya na ci gaba da alhinin kisan jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka kashe a hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai kan Iran.

    Ayatollah mai shekara 86 na da matuƙar tasiri a Iran da ma ƙasashen duniya, musamman tsakanin mabiya aƙidar Shi'a a faɗin duniya

    Tuni dai mabiya ƙungiyar ƴan'uwa Musulmi a Najeriya ta ,yan Shi'a suka shiga jimaminsa ta hanayr gudanar da taron muzaharori da zanga-zangar lumana domin bayyana alhininsu.

    Malam Sidi Mannir Mainasara ɗaya daga cikin manyan almajiran Sheikh Alzakzaky kuma wanda ya san rayuwar Ayatoullah Ali Khamenei, ya bayyana wa BBC yadda mabiya shi'a a faɗin duniya suka ji da rashinsa.

    Ya ce kisan Ayatollah ya ƙara fito da martaba da tasirin aƙidar Shi'a ke da shi a Najeriya.

    ''Za ka sha mamaki idan ka ga yadda mutane suka ajiye bambancin aƙida suka riƙa yi mana ta'aziyyar rasuwarsa'', in ji shi.

    Ya ci gaba da cewa abin ya ba su mamaki, yadda mutuwarsa ta mantar da al'umma bambancin aƙida.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.