Mutum 39 sun mutu a hatsarin jirgin ƙasa a Sifaniya

Asalin hoton, Reuters
Akalla mutum 39 sun rasa ransu sannan wasu da dama sun jikkata bayan wasu jiragen ƙasa biyu sun yi taho mu gama da juna a kudancin Sifaniya.
Ɗaya daga cikin jiragen na kan hanyarsa ne daga Malaga zuwa Madrid inda ya kauce wa hanyarsa, ya koma kan ɗaya layin dogon da a nan ne suka yi karo da wani jirgin da ke tafiya a kan layin dogon.
Firaiministan Sifaniya, Pedro Sanchez ya bayyana lamarin a matsayin abin tashin hankali da kaɗuwa.
Ministan harkokin sufuri na ƙasar ya ce har yanzu ba a san dalilin da ya sa jirgin ya kauce daga hanyarsa ba.
Tuni dai masu aikin ceto suka ce kai wa ga waɗanda suka makale a cikin jirgin na wahala saboda yadda jiragen suka lotse.

