Gwamnatin Venezuela za ta ba da lada ga duk wanda ya faɗi inda jagoran adawa yake
Gwamnatin Venezuela ta sanar da cewa za ta bayar da tukwicin dala 100,000 ga duk wanda ya bayar da bayanan da za su kai ga kama jagoran 'yan'adawar ƙasar da ya yi gudun hijira.
Edmundo Gonzales ya tsere daga ƙasar a watan Satumban bara kuma ya samu mafaka a Sifaniya bayan mahukuntan ƙasar sun bayar da umarnin kama shi.
Sai dai ya yi alƙawarin komawa wa Caracas kafin a rantsar da Shugaba Nicolas Maduro a ranar Juma'a mai zuwa, inda ya zargi gwamnati da maguɗin zaɓe.



