An kashe mutane biyu a zanga-zangar matasa a Morocco

Asalin hoton, AFP via Getty Images
'Yansanda sun bude wuta domin tarwatsa masu zanga-zanga da ke kokarin farwa wani caji ofis a Lqliaa a kusan da birnin Agadir mai tashar ruwa a kasar Morocco, lamarin da ya hallaka mutum biyu.
Wannan ne karon farko da aka samu rasa rai tun bayan fara zanga-zangar da matan Gen-Z suka fara, kan matakin gwamnati na gina filin wasan kwallon kafa domin gasar cin kofin duniya ta shekarar 2030, maimakon inganta rayuwar yan kasa da magance tabarbarewar tattalin arziki.
Masu zanga-zangar na cewa kasar na da filayen wasa da dama, amma babu wadatattun asibitoci. Wani mai zanga-zanga ya shaidawa BBC asibitin birninsu Oujda da ke iyakar kasar da Algeria ya lalace, ya fi kama da kurkuku maimakon asibiti.
Masu zanga-zangar na zargin jami'an tsaro da ma'aikatan jinya a asibitocin gwamnati da karbar na goro a hannun marasa lafiya kafin su samu ganin likita.
Ana dai gudnar da zanga-zangar a kowanne dare, inda 'yansandan Morocco ke cewa tilas su ke bude wuta a sama domin tarwatsa masu zanga-zangar. Ko a jiya Laraba 'yansandan sun bude wuta a sama domin kare kai lokacin da aka kai musu hari, kamar yadda kafar yada labaran birnin Lqliaa ta rawaito.
















