Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 11/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 11 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • Iran na gudanar da jana'izar manyan kwamandojinta
  • Kotu ta ba mu damar ci gaba da tsare El-Rufai - ICPC
  • Iran ta yi barazanar kai hari kan bankunan Amurka da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya
  • An kai hare-haren jirage marasa matuƙa kan wuraren Amurka a Iraq
  • Dangote ya rage farashin man fetur
  • Iran ta kai 'hari mafi muni' kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka
  • Amurka ta ce ta lalata jiragen Iran 16 masu sanya nakiyoyi a Hormuz
  • Za mu ɗauki duk wanda a fito zanga-zanga a matsayin maƙiyi - Iran
  • Me ya sa shugaban Iran ya nemi afuwar maƙwaftan ƙasar?

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza

Assalamu alaikum

Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.