Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 30/09/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 30/09/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Babangida

  1. MDD ta gargadi ƙasashen Afirka kan fuskantar haraji bayan ƙarewar AGOA

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Taron Majalisar Dinkin Duniya kan kasuwanci da cigaba, UNCTAD, ta yi gargaɗi cewa ƙasashen Afirka na fuskantar barazanar ƙarin haraji da rage damar shiga kasuwannin Amurka, bayan ƙarewar yarjejeniyar bunƙasawa da bai wa ƙasashen afrka dama ta AGOA a yau Talata.

    Shirin AGOA, wanda aka shafe tsawon shekaru 25 ana amfani da shi, ya bai wa ƙasashen Afirka kusan 30 damar fitar da kayayyaki zuwa Amurka ba tare da biyan haraji ba.

    Sai dai yanzu, yayin da Amurka ke nazarin yiwuwar tsawaita yarjejeniyar, dubban ‘yan Afirka na fuskantar barazanar rasa ayyukansu, musamman ma a masana’antar kayan ɗinki da tufafi.

    Shirin AGOA dai an fara shi a majalisar dokokin Amurka ne a shekarar 2000, domin ƙarfafa ciniki da jari tsakanin Amurka da ƙasashen Afirka.

    An sabunta shi a shekarar 2015, inda aka ƙara masa shekaru goma.

    Yanzu kuwa, kamfanoni da dama a nahiyar sun shiga halin rashin tabbas kan makomar tattalin arzikinsu.

  2. Ƴan Najeriya ba su manta 'munin' mulkin Jonathan ba - Fadar shugaban ƙasa

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan na da ‘yancin tsayawa takarar shugabancin ƙasar a shekarar 2027.

    Sai dai ta jaddada cewa ‘yan Najeriya ne za su yi masa hukunci saboda ba su manta 'munin' mulkin Jonathan ba, ta kuma kwatanta mulkin Tinubu da abin da ta bayyana a matsayin “gagarumin ci gaban tattalin arziƙi”

    Fadar shugaban ƙasar ta kuma ɗora alhakin fara yaƙin neman zaɓe da wuri kan masu neman kifar da shugaba mai ci.

    Hakan na zuwa ne a rana guda da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ba za ta bai wa Jonathan tikitin tsayawa takara kai tsaye ba, inda ta bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin “zaɓuɓɓukan da take dubawa.

  3. Bikin Ƴancin kai: Gwamnatin Najeriya ta soke faretin ƙasa

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin tarayya ta soke bikin faretin da aka shirya gudanarwa domin murnar cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai a ranar Laraba, 1 ga watan Oktoba.

    Wannan sanarwar ta fito ne a ranar Litinin daga Ofishin sakataren gwamnatin tarayya.

    “Soke faretin bikin ƴancin kai da gwamnati ta shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 ga Oktoba ba zai rage darajar wannan muhimmiyar rana ta tarihi ba,” in ji sanarwar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnati na ba da haƙuri kan wannan sauyi, amma sauran ayyukan da aka tsara domin zagayowar ranar za su ci gaba kamar yadda aka tsara.

    Wannan ya haɗa da jawabin shugaban ƙasa, bukukuwan al’adu, da wasu abubuwa da aka shirya.

  4. Cikar Najeriya shekara 65: Gwamnatin Najeriya ta bayar da hutun ranar Laraba

    Tinubu zaune a ofishinsa

    Asalin hoton, Fadar shugaban Najeriya

    Gwamnatin Najeriya ta sanar da gobe Laraba a matsayin ranar hutu a ƙasar somin bikin cikar ƙasar shekara 65 da samun ƴancin kai.

    Cikin wata sanarwa da ministan cikin gida na ƙasar, Olibunmi Tunji-Oja ya fitar, ya taya ƴan Najeriya murnar cimma wannan ''babban matsayi''.

    Ministan ya kuma buƙaci ƴanƙasar su ci gaba da nuna kishin ƙasa da hadin kai da juriya, waɗanda ya ce su ne ke taimaka wa ƙasar wajen dunƙulewa tun lokacin samun ƴancin kai a 1960.

    A ranar 1 ga watan Otoban 1960 ne dai Najeriya ta samun ƴancin kai daga Turawan mulkin Birtaniya da suka yi mata mulkin mallaka.

  5. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana da Talata.

    Barkanmu da sake haɗuwa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Kuna iya bibiyarmu a shafukanmu da sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.