Yanzu ake buga Premier League - Guardiola, Premier League

Asalin hoton, Getty Images
Pep Guardiola ya ce yanzu ne aka fara buga Premier League ya kuma ce yana sa ran za a ga karin abubuwan da za suke ɗaukar hankali a kokarin lashe kofin bana, ya jaddada cewa Manchester City ba za ta mika wuya ba wajen ci gaba da kalubalantar Arsenal ba.
Ƙungiyar da Guardiola ke jan ragama ta ci gaba da matsawa Arsenal lamba wajen maye gurbinta a kan teburin kakar bana.
Ranar Asabar City ta doke Newcastle 2-1 a Etihad a wasan mako na 27, kenan saura maki biyu tsakani da Arsenal mai jan ragama, wadda za ta fafata da Tottenham a wasan mako na 28 ranar Lahadi.






