Najeriya da Masar za su fafata a wasan neman matsayi na uku a Afcon karo na 32.
A cikin wasa 31 da aka buga a baya a neman matsayi na uku an ci ƙwallo 87.
A cikin wasa 13 daga 31, dukkan tawagogin biyu sun ci kwallo.
Wasa biyar baya a gurbin neman mataki na uku da fenariti aka kare — 1988, 1998, 2000, 2015 da 2023.
Wasan neman mataki na uku da aka fi cin ƙwallaye shi ne na 1998, lokacin da Burkina Faso da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DR Congo) suka tashi 4–4, inda DR Congo ta yi nasara a bugun fenariti bayan Burkina Faso ta fara da cin ƙwallo 3–0 da kuma 4–1.