Sojoji sun kuɓutar da mutum 86 da aka yi garkuwa da su a Borno

Asalin hoton, Other
Rundunar sojin ƙasan Najeriya ta ce sojojinta sun samu nasarar kuɓutar da mutum 86 daga masu garkuwa da mutane, sannan ta kama ƴanbiniga da masu taimaka musu guda 29 a sassa daban-daban na jihar Borno da ke arewa maso gabas.
A wata sanarwa da kakakin aikin soji na musamman na Hadin Kai, Sani Uba ya fitar, ya ce sojojin bataliya ta musamman ta 135 a ƙarƙashin sashe na 2 ne suka yi artabu da ƴan Boko Haram a ranar 9 ga watan Nuwamba a yankin Dutse Kura.
"Ƴan Boko Haram sun kai hari ne kan matafiya a hanyar Buratai zuwa Kamuya. Nan ne sojojinmu suka kai ɗauki, wanda ya sa maharan suka tsere, amma sai sojojin suka bi bayansu a hanyar zuwa Mangari har suka ci ƙarfinsu," kamar yadda sanarwar ta nuna.
Ya ce daga bisani sojojin sun baza ƙomarsu a dazukan, inda suka samu nasarar gano sansanin mayaƙan guda 11, "inda muka ceto mutum 86 ciki har da mata da ƙananan yara, sannan muka ƙwato bindigar AK-47 da harsasai da sauran makamai."


