Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 04/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 4 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

  • Za mu ɗauko ƙwararru daga China domin inganta matatun man Najeriya - NNPCL
  • Gwamnatin Sokoto ta rage aƙalla kashi 60 a farashin takin zamani ga manoman jihar
  • An fara bincike kan kisan Saif al-Islam Gaddafi
  • Saudiyya za ta fara bai wa raƙuman ƙasarta fasfo
  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • Najeriya ta tabbatar da zuwan sojojin Amurka ƙasar
  • Yarjejeniyar taƙaita amfani da nukiliya tsakanin Amurka da Rasha za ta ƙare a yau
  • Har yanzu majalisar dattawa ba ta kammala gyaran dokar zaɓe ba
  • Ukraine da Rasha za su fara tattaunawar zaman lafiya a Abu Dhabi
  • Sojojin Sudan sun ƙwace birnin kudancin ƙasar daga hannun RSF
  • WFP ya dakatar da ayyukansa a wasu sassan jihar Sudan ta Kudu
  • Nawa jihohin Najeriya ke samu daga tarayya kuma yaya suke kashe kuɗin?
  • Ƙasashen da azuminsu zai fi tsawo a 2026

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed, Aisha Babangida da Ahmad Bawage

  1. Nawa jihohin Najeriya ke samu daga tarayya kuma yaya suke kashe kuɗin?

    ...

    Asalin hoton, Fadar shugaban ƙasa/X

    Ƴan Najeriya sun ci gaba da muhawara kan maƙudan kuɗaɗen shiga da matakan gwamnati uku suka raba a Najeriya cikin watan Janaurin da ya gabata.

    Hukumar raba arzikin ƙasar, FAAC ta ce matakan gwamnatin uku, wato gwamnatin tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukukomi sun raba naira tiriliyan 1. 963 a watan da ya gabatan.

    Cikin wata sanarwar darakta yaɗa labaran ofishin babban akanta na ƙasa , Bawa Mokwa ya fitar a farkon makon da muke ciki ya ce an samu nasarar tara kuɗaɗen ne ta hanyar harajin cikin gida da aka tara a watan na naira tiriliyan 1.08 da kuma naira biliyan 846.507 da aka tara daga harajin VAT, sai kuma naira biliyan 38.110 da aka tara daga harajin tura kuɗaɗe ta intanet.

    Sanarwar ta ce bayan kasafta kuɗaɗe gwamnatin tarayya ta samu naira biliyan 653.500, yayin da jimillar jihohin ƙasar 36 da birnin Abuja suka samu naira biliyan 706.469, sai kuma ƙananan hukumomi da suka samu naira biliyan 513.272.

  2. Ukraine da Rasha za su fara tattaunawar zaman lafiya a Abu Dhabi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana sa ran Ukraine da Rasha za su fara tattaunawa ta tsawon kwanaki biyu nan ba da jimawa ba, domin cimma yarjejeniyar zaman lafiya, a birnin Abu Dhabi.

    Tattaunawar dai Amurka ce ta shirya ta, a wani yunƙuri na kawo ƙarshen yakƙn da ke ci gaba da gudana tsakanin ƙasashen biyu.

    A jiya Talata, Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya zargi Rasha da zaɓar yaƙi maimakon zaman lafiya, biyo bayan sabon harin da aka kai wa ƙasarsa.

    Ya kuma yi kira da a ƙara matsa wa Rasha lamba a duniya, domin tilasta mata amincewa da yarjejeniyar zaman lafiya.

    Sai dai a halin yanzu, Ukraine na fuskantar matsin lamba daga Amurka, wadda ke buƙatar ta sassauta matsayinta ta hanyar miƙa wasu yankunanta da aka ƙwace a gabashin yankin Donbas, domin cimma zaman lafiya.

  3. Amurka ta sabunta yarjejeniyar kasuwanci da ƙasashen Afirka 32

    Amurka

    Asalin hoton, Reuters

    Amurka ta sabunta yarjejeniyar kasuwanci da zai bai wa ƙasashen Afirka 32 damar fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin ƙasar ba tare da biyan haraji ko fuskantar shingayen kasuwanci ba.

    Yarjejeniyar, wadda aka cimma tun shekaru 25 da suka gabata, ta kare ne a watan Satumbar bara.

    Sai dai yanzu gwamnatin Amurka ta tsawaita wa’adinta har zuwa ƙarshen shekarar da muke ciki ta 2026, domin bai wa ƙasashen Afirka damar ci gaba da cin gajiyar wannan tsari.

    Ministan kasuwanci na Amurka ya bayyana cewa za su yi aiki kafada da kafada da ’yan majalisar dokokin ƙasar, domin sake duba yarjejeniyar tare da yi mata garambawul, ta yadda za ta fi dacewa da sauye-sauyen da ke faruwa a harkokin kasuwancin duniya.

    Masana na ganin wannan tsawaitawa za ta taimaka wajen tallafa wa tattalin arzikin ƙasashen Afirka, musamman wajen ƙara fitar da kayayyaki da samar da ayyukan yi da kuma ƙarfafa alaƙar kasuwanci tsakanin Afirka da Amurka.

  4. Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.