An haramta wa ƴara buɗe shafukan sada zumunta a Malaysia

Asalin hoton, Getty Images
Malaysia ta fara hana ƴan ƙasa da shekara 16 daga buɗe shafukan sada zumunta.
Hukumar kula da harkokin sadarwa ta ƙasar ta ce dole ne shafuka kamar Fesbuk da Instagram da Tikok da YouTube su tantance shekaru kan bayanan gwamnati da aka bayar.
Malaysia ta bi sahun ƙasashen da suka bijiro da matakai makamancin haka domin kare yara daga ganin abubuwan da ba su kamata ba a shafukan sada zumunta.
Kamfanonin da suka gaza martaba matakin zai fuskanci tarar kusan dala miliyan biyu da rabi.














