Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 19/06/2025.

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi da Aisha Babangida

  1. Bidiyon ɓarnar da harin Iran ya yi wa ciki da wajen asibitin Isra'ila a Beersheba

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon
  2. Isra'ilawa na ɗaga ɓaraguzai don neman waɗanda suka maƙale bayan harin Iran

    Wasu gine-gine da suka ruguje

    Asalin hoton, EPA

    Hukumomin Isra’ila sun ce mutum uku sun jikkata sosai sakamakon harin makami mai linzami da Iran ta harba zuwa yankin a baya-bayan nan.

    Harin ya lalata gine-gine ciki harda asibitin Soroka na Isra'ila, lamarin da ya sa Isra'ilawa da ƴan sanda da ma'aikatan ceto ke ɗaga ɓaraguzai don neman waɗanda suka maƙale bayan harin na Iran

    Wani mutum, wanda harin da makamai masu linzami da Iran ta kai ya rushe masa ɗaki ya samu ya tsere.

  3. Wane bom mai ƙarfi na Amurka ne zai iya lalata rumbunan nukiliyar Iran?

    ...

    Asalin hoton, US Air Force

    Daga cikin makaman da za a iya harbawa su keta ƙarƙashin ƙasa har su iso wurin da rumbunan ajiyar sinadaran nukiliyar Iran suke, daya ne kawai ba a yi amfani da shi ba zuwa yanzu, kuma Isra'ila ba ta da shi a yanzu.

    Makamin shi ne GBU-57A/B - wanda ya kasance bom marar nukiliya mafi ƙarfi a duniya - da zai iya lalata rumbunan ajiyar sinadaran ƙera makamin nukiliya, kuma Amurka ce kadai ta mallake shi a duniya.

    Wannan tsararren makami mai nauyin kilogiram 13,600 zai iya ketawa ƙarƙashin ƙasa domin wargaza rumbunan sinadaran ƙera nukiliyar Iran da ke binne can ƙarƙashin duwatsu.

    Zuwa yanzu Amurka ba ta bai wa Isra'ila makamain ba.

    To amma shi wannan makami ya yake, mene ne kuma ƙalubalen amfani da shi.

  4. Hotunan ɓarnar da harin Iran kan Isra'ila ta haddasa

  5. Harin Iran ya lalata wani asibiti a Isra'ila