Za mu fitar da matsayarmu kan ko za mu shigar wa Isra'ila yaƙi nan da mako biyu - Trump
Shugaba Trump ya ce sai nan da mako biyu zai yanke hukunci kan ko zai shigar wa Isra'ila yaƙin da take yi da Iran ko kuma akasin haka.
A wata sanarwa da sakatariyar yaɗa labaran fadar gwmanatin Amurka ta karanto, Shugaban ya ce akwai yiwuwar a zauna a teburin sulhu.
Kafin wannan sanarwa, mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Saeed Khatib-zadeh ya fada wa BBC cewa ba su da matsalar tattaunawar diflomasiya idan aka daina jefa musu bama-bamai.
Ya kuma ce duk da Iran a shirye take ta shiga tattaunawar diflomasiya - babu batun ragawa Isra'ila.
Kuma illahirin yankin zai shiga cikin bala'i muddin Amurka ta yi ƙoƙarin shiga yaƙin.