Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Labaran wasannin BBC Hausa kai-tsaye daga 2 zuwa 8 ga watan Agustan 2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Asabar 2 ga watan Agusta zuwa 1 ga watan Agusta 2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu, Abdulrazzaq Kumo, da Umar Mikail

  1. Everton ta saye ɗan wasan tsakiya daga Chelsea

    Everton ta amince ta saya ɗan wasan tsakiya Kiernan Dewsbury-Hall daga Chelsea kan fam miliyan 28.

    Everton za ta biya miliyan 24 kai tsaye amma za ta ƙara miliyan uku zuwa huɗu idan ya taka rawar gani.

    Dewsbury-Hall dai bai so barin Chelsea ba duk da cewa ba ya buga wasanni da yawa a ƙungiyar da ta lashe kofin Club World Cup.

    Sai dai Chelsea ba ta damu ta rabu da ɗan wasan ba idan har aka biya ta kusa da miliyan 30 - farashin da ta ɗauke shi.

  2. Tinubu ya ba ƴan wasan kwandon Najeriya mata dala 100,000 da lambar girma

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ba ƴan wasan kwandon Najeriya mata dala 100,000 da lambar girma ta OON saboda nasarar da suka samu ta lashe kofin gasar kofin Afirka ta wato Afrobasket.

    Shugaban ya kuma ba masu horar da ƴanwasan dala 50,000 kowannensu.

    A ranar Lahadi ne tawagar D’Tigress ta lashe gasar ƙwallon kwando ta matan Afirka, bayan doke Mali da ci 78-64, lamarin da ya zama karo na bakwai da tawagar Najeriya ta lashe kofin gasar a tarihi, kuma shi ne na biyar a jere.

  3. Tawagar D'Tigress ta Najeriya ta isa gida bayan lashe kofin Afirka

    Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando ta mata ta Najeriya ta koma ƙasar bayan lashe gasar ƙwallon kwando ta mata ta Afirka.

    Tawagar ta D’Tigress ta samu gagarumar tarba daga masoya ƙwallon kwando a Najeriya, lokacin da suka sauka a filin jirgin sama na Abuja.

    A ranar Lahadi ne tawagar D’Tigress ta lashe gasar ƙwallon kwando ta mata ta Afirka, bayan doke Mali da ci 78-64.

    Wannan ne karo na bakwai da tawagar Najeriya ta lashe kofin gasar a tarihi, wanda kuma shi ne na biyar a jere da ta ɗauka.

  4. Me ya sa Madrid ke son sayar da Rodrygo?

    Akwai yiwuwar cewa Rodrygo zai taka leda a Gasar Premier Ingila a kaka mai zuwa yayin da wasu ƙungiyoyi ke nuna sha'awar ɗaukar ɗan wasan, ita kuwa Real Madrid a shirye take ta sayar da shi.

    Ɗan wasan bai taka rawar gani a kakar da aka kammala ba kuma ya zura ƙwallo ɗaya ne kawai cikin wasanni 22 tun daga watan Fabrairu zuwa yanzu.

    An kuma fitar da shi a hutun rabin lokaci a wasan ƙarshe na gasar Copa del Rey a kakar - lamarin da bai cika faruwa ba.

    Bayan zuwan sabon koci Xabi Alonso ƙungiyar, Rodrygo ya kasa samun damar buga wasa inda wasa ɗaya kaɗai ya fara cikin shida a gasar Club world Cup.

    Rodrygo ya bayar da ƙwallo aka ci a wasansu da Al-Hilal, amma idan yana buga gefen dama, shi da Alexander-Arnold na kawo cikas a ɓangaren tsaron bayan Real Madrid.

    Ɗan wasan kuma ya fi son buga gefen hagu inda Vinicius har da ma Mbappe suka fi son bugawa, duk da cewa Mbappe ma lamba tara yake bugawa.

    Yawan ƙwallayen da ya ci a kakar da aka kammala bai kai na Mbappe da Vinicius yawa ba duk da cewa a wasu alƙaluma irin ƙwace ƙwallo, ya fi ƴan wasan biyu.

  5. Tottenham ta ɗauki Joao Palhinha daga Bayern Munich

    Tottenham ta kammala ɗaukar Joao Palhinha daga Bayern Munich a matsayin aro.

    Ɗan wasan na Portugal ya je Bayern ne daga Fulham a 2024 amma bai samu damar buga wasanni da yawa ba inda ya buga wasanni 17 kaɗai.

    Kocin Spurs Thomas Frank ya nace ƙungiyar ta ɗauki ɗan wasan tsakiyar saboda akwai yiwuwar Yves Bissouma da Rodrigo Bentancur za su bar ƙungiyar.

    Palhinha ya saba da gasasr Premier inda ya buga wasa 68 cikin kaka biyu a Fulham.

    Shi ne kuma ɗan wasa na uku da Tottenham ta ɗauka bayan Mohammed Kudus da Mathys Tel.

  6. 'Dole Isak ya ƙasƙantar da kai kafin ya dawo atisaye da Newcastle'

    Ɗan wasan mai shekara 25 da ya nuna aniyarsa ta barin ƙungiyar a watan Yuli, baya cikin tawagar da ke buga wasannin share fage a nahiyar Asiya saboda "ciwon ƙafa".

    Isak ya dawo atisaye a filin Newcastle ranar Litinin, amma koci Eddie Howe ya ce bai yi magana da ɗan wasan ba tun bayan da Liverpool ta miƙa tayi.

    "Matsayinsa ɗaya da kowane ɗanwasa, muna sa ran zai dawo atisaye kamar kowa," inji Eddie Howe. "Dole sai ka cancanci yin atisaye da mu" ya ƙara.

    Eddie Howe ya ce babu wani ɗan wasa a ƙungiyar da ya isa ya nuna hali maras kyau ya kuma yi tunanin zai ci gaba da yin atisaye tare da kowa.

  7. Barcelona ta zazzaga wa Daegu FC ƙwallo biyar

    Barcelona ta kammala wasannin share fage da ta gudanar a Koriya ta Kudu a bana, da nasara kan Daegu da ci 5-0 a yau Litinin.

    Sabon ɗan wasan ƙungiyar, Marcus Rashford ya zura ƙwallonsa na farko a ƙungiyar, sannan Gavi ya zura biyu, Lewandoski da Toni Fernandez suka zura sauran.

    Barca za ta kammala shirye-shiryen kaka mai zuwa a wasanta na lashe kofin Joan Gamper da za ta yi da Como ranar 10 ga watan Augusta, sannan ta buga wasanta na farko a gasar La Liga da Mallorca ranar 16 ga watan.

  8. Yadda Tottenham ta yi ban kwana da Son

    Bayan wasan Son Heung-min na ƙarshe da Tottenham, abokan wasansa sun cilla shi sama, yayin da magoya baya suka riƙa tafawa domin jinjina masa.

    Son ya fara tattaunawa da ƙungiyar Los Angeles FC kuma ana sa ran za a saye shi kan fam miliyan 20.

    Ɗan wasan ya kuma zubar da hawaye bayan ganin ƙaunar da aka nuna masa, ya ce "barin Tottenham, ƙungiyar da na yi shekara 10 da, mataki ne mai tsauri a wurina."

  9. Ƙungiyar D’Tigress ta Najeriya ta lashe Gasar ƙwallon kwandon Afirka, FIBA

    Ƙungiyar D’Tigress ta Najeriya ta kafa tarihin zama ta farko da ta taɓa lashe Gasar ƙwallon kwandon Afirka, FIBA sau biyar a jere

    Tawagar ta samu nasara ne a wasan ƙarshe bayan doke Mali da ci 78-64 domin lashe gasar, karo na bakwai a tarihi.

    Wannan nasarar na nufin za su je Gasar ƙwallon kwando ta duniya da za a yi a 2026 a birnin Berlin.

    Ƴan wasan Najeriyar sun kankane Gasar ƙwallon kwandon Afirka, inda suka yi nasara sau 29 a jere a duka wasan da suka buga ba tare da rashin nasara ba tun 2015.

    D’Tigress na komawa gida Najeriya daga birnin Abidjan na ƙasar Ivory Coast, inda za su haɗu da shugaban Najeriya Bola Tinubu don kai masa kofin da suka lashe.

  10. Labarai da dumi-dumi, Chelsea ta sayi Hato kan fam miliyan 37 daga Ajax

    Chelsea ta kammala sayen ɗan wasan Ajax mai tsaron baya, Jorrel Hato kan fam miliyan 37.

    Mai shekara 19 ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka bakwai da ƙungiyar Stamford Bridge, bayan da aka kammala auna koshin lafiyarsa a Landan a karshen mako.

    Ɗan wasan tawagar Netherlands ya zama na ta takwas da Chelsea ta ɗauka, wadda take rike da Fifa Club World.

  11. Kociyan Tottenham, Thomas Frank ya ce daga ganin raunin da James Maddison ya ji a lokacin karawar sada zumunta da Newcastle United zai yi muni.

    Dan wasan mai shekara 28 ya ji raunin ne a wasan da suka tashi 1-1 da Newcastle United ranar Lahadi a birnin Seoul a Koriya ta Kudu.

    Daga baya sai sauya dan kwallon tawagar Ingila aka yi, kuma a karawar ce ƙyaftin Son Heung-min ya yi ban kwana da magoya baya.

    Ana sa ran Son zai koma taka leda a Amurka da Los Angeles FC.

  12. Lookman ya zargi Atalanta da saɓa alkawari

    Ɗan wasan tawagar Najeriya, Ademola Lookman ya ce ya mika batun neman izinin barin Atalanta, bayan da ya zargi ƙungiyar da saɓa alkawari.

    Mai shekara 27, wanda Inter Milan ke son ɗauka ya ce mahukuntan Atalanta sun amince ya bar ƙungiyar idan ya samu tayi mai tsoka.

    Lookman ya kara da cewar ƙungiyar sai ta kasa cika alkawari, wadda ta toshe duk wata kafar da ya kamata ya bar Atalanta.

    Ɗan wasan tawagar Najeriya ya koma Atalanta daga RB Leipzig a 2022.

    Lookman ya ci ƙwallo 52 a wasa 117 a ƙungiyar dake buga Serie A.

  13. Son ya yi ban kwana da Tottenham a Seoul

    Son Heung-min ya yi ban kwana da Tottenham a gaban dubban magoya baya a birnin Seoul a Koriya ta Kudu.

    Ƴan Tottenham da na Newcastle da suka buga wasan sada zumunci duk sun rungumi ɗan wasan suna taya shi murna, wanda aka sauya shi a minti na 65.

    Lokacin da zai fita daga fili ya mika ƙyallen ƙyaftin ga Ben Devies, kuma lokacin da zai je wajen ƴan zanman benci sun mike suna yi masa tafin girmamawa.

    Son ya zama ɗan wasan Nahiyar Asia da aka saya mafi tsada a Premier League a tarihi lokacin da ya koma Tottenham daga Bayer Leverkusen kan fam miliyan a 2015.

    A watan Mayu ya ja ragamar Tottenham ta lashe Europa League, sakamakon nasara a kan Manchester United.

    Hakan ya kawo karshen shekara 17 rabonta da lashe babban kofi.

    Son yana tattaunawa da Los Angeles FC a shirin komawa buga gasar ƙwallon kafar Amurka.

  14. Kenya ta fara da cin Jamhuriyar Congo a Chan

    Kenya ta fara gasar cin kofin nahiyar Afirka ta ƴan wasan dake taka leda a nahiyar wato Chan da kafar dama, bayan da ta doke Jamhuriyar Congo da ci 1-0 ranar Lahadi.

    Austin Odhiambo ne ya ci kwallon a wasan da aka buga a Kenya a karawar farko ta ƴan rukuni na ɗaya.

    Ana buga Chan a duk bayan shekara biyu, inda ake bai wa yan kwallon dake taka leda a gida, domin su nuna bajintarsu

    Ranar Alhamis Kenya za ta buga wasan gaba da Angola, ita kuwa Jamhuriyar Congo mai Chan biyu a tarihi za ta kece raini da Morocco a dfaya was an rukunin farko.

    Sai a ranar Talata Najeria za ta fafata da Senegal mai rike da kofin a wasan rukuni na hudu kafin nan sai a barje gumi tsakanin Congo da Sudan.

    A karon farko ana buga Chan na bana Kenya da Uganda da Tanzaniya.

  15. Newcastle United ta gabatar da tayin fam miliyan 65.3 kan ɗan wasan Slovenia da RB Leipzig, Benjamin Sesko mai shekara 23. (Sky Sports)

    Manchester United na tattaunawa ita ma da Sesko, wanda har yanzu bai yanke hukunci ba kan zaɓin tafiya Manchester United ko Newcastle. (Fabrizio Romano)

    Liverpool za ta sake gabatar da tayi kan ɗan wasan Sweden Alexander Isak mai shekara 25, idan Newcastle ta samu mai maye gurbinsa.. (Daily Mail)

    Arsenal na nazari kan Isak kafin ta cimma yarjejeniya da Viktor Gyokeres amma tana nuna shaku kan ɗan wasan gaban a Newcastle. (ESPN)

  16. Tawagar Brazil ta mata ta kare lashe Copa America

    Tawagar ƙwallon kafa ta mata ta Brazil ta kara lashe Copa America a bugun fenariti bayan nasara a kan Colombia.

    An buga karawar ta hamayya a birnin Quito a Ecuador.

    Kowacce tawaga ta ci ƙwallo huɗu a bugun fenariti daga baya mai tsaron ragar Brazil, Lorena ta tare ƙwallon da Jorelyn Carabali ta buga mata.

  17. CHAN: Afirka ta Kuda ta sauka a Uganda ranar Lahadi

    Da sanyin safiyar Lahadi tawagar Afirka ta Kudu ta sauka a birnin Kampala a Uganda, domin buga wasannin cin kofin Afirka ta ƴan wasan dake taka leda a gida.

    Afirka ta Kudu tana rukuni na uku da ya haɗa da Uganda da Niger da Guinea da kuma Algeria.

  18. Mboko ta yi waje da Gauff a Canadian Open

    Matashiya, Victoria Mboko ta yi waje road da Coco Gauff ta kuma kai kwata fainal a Canadian Open a Montreal.

    Mai shekara 18 ta yi nasara a kan mai Grand Slam biyu da cin 6-1 6-4.

    Itama Iga Swiatek ta kai zagayen ƴan 16, bayan doke Eva Lys da ci 6-2 6-2.

    Shi kuwa Casper Ruud ya sha kashi da ci 6-4 7-5 a hannun Karen Khachanov, Alexander Zverev ma ya kai kwata fainal, bayan doke Francisco Cerundolo.

  19. An kammala duba lafiyar ɗan wasan baya a Netherlands Jorrel Hato mai shekara 19 a Chelsea kan cimma yarjejeniyar fam miliyan 35.5 a kansa. (Sky Sports)

    Manchester United na shirin gabatar da tayin fam miliyan 16 kan ɗan wasan Barcelona da Sifaniya mai shekara 22, Fermin Lopez. (Sport - in Spanish)

    AC Milan na tattaunawa ɗan wasan Liverpool da Uruguay, Darwin Nunez mai shekara 26, kan komawarsa San Siro amma kuma akwai Al-Hilal da take zawarcinsa ido rufe. (Sky Sports Italia - in Italian)

    Crystal Palace ta gaza a cimma yarjejeniyar fam miliyan 28 kan ɗan wasan Inter Milan da Jamus, Yann Bissek mai shekara 24. (Gazzetta Dello Sport - in Italian, external)

  20. CHAN: Wasa uku za a buga ranar Lahadi

    Wasa uku za a buga a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta ƴan ƴan ƙwallon dake taka leda a gida da ake yi a Kenya da Tanzaniya da kuma Uganda.

    Rukunin farko za a fafata tsakanin Kenya da Jamhuriyar Congo da na Morocco da Angola.

    Yayin da wasa ɗaya za a buga a rukuni na biyu shi ne tsakanin Madagasca da Mauritania