Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 22/10/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 22/10/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Muhammad Annur da Isiyaku Muhammed

  1. Putin zai gana da ƙawayen Rasha domin nuna wa ƙasashen yamma ƙwanji

    Ka kwatanta kanka a matsayin Vladimir Putin.

    Ƙasashen yamma suna maka ƙiyayya saboda ƙaddamar da yaƙi a Ukraine. Sannan an ƙaƙaba maka wasu takunkumi domin hana tattalin arzikin ƙasarka takaɓus a kasuwannin duniya.

    Sannan kotun manyan laifuka ta bayar da umarnin a kama ka da zarar ka bar ƙasarka.

    Ta yaya ne za ka iya nuna wa ƙasashen nan ƙwanji? sai kawai ka gwada shirya wani babban taro.

  2. Hukunci 10 da kotu ta yanke kan zaɓen ƙananan hukumomi a jihar Kano

    A ranar Talatar nan ne wata babbar Kotun tarayya a kano ƙarƙashin jagorancin mai shari'a Simon Amobeda ta rushe shugabancin hukumar zaɓe ta jahar Kano bisa dogaro da hujjojin da aka gabatar mata na rashin cancantar shugabannin hukumar bisa kasancewarsu ƴan siyasa masu ɗauke da katin Jam'iyyar NNPP.

    Wani ɗan jam'iyyar APC Hon Aminu Tiga da Jam iyyarsa ta APC ne dai suka shigar da ƙara inda suka roƙi kotun da ta rushe shugabannin hukumar zaɓen ta Kano bisa kasancewrsu ƴan jam'iyya mai mulki.

  3. Hezbollah ta ɗauki nauyin kai harin jirgi maras matuƙi gidan Netanyahu

    Ƙungiyar Hezbollah ta ce ita ce ta kai harin jirgi maras matuƙi kan gidan shaƙatawa na Benjamin Netanyahu a makon da ya gabata a garin Caesarea da ke bakin ruwa.

    Ƙungiyar ta tabbatar da hakan ne yayin wani taron manema labarai a ɗazu wanda aka tarwatsa shi bayan sanarwar da dakarun Isra'ila suka fitar cewa kowa ya bar wurin za su kai hari.

    Mai kula da ofishin ƙungiyar a harkar yaɗa labarai, Mohammed Afif ne ya faɗi hakan.

    A makon da ya gabata ne dai wani harin jirgi maras matuƙi ya rusa wani ɓangare na gidn shaƙatawar na Benjamin Netanyahu duk da cewa babu wani da ya samu rauni.

    A lokacin Benjamin Netanyahu ya ɗora alhakin harin kan Hezbollah, a shafinsa na X

    Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya rawaito Afifi na cewa "Hezbollah ta ɗauki alhakin harar gidan na firaiministan Isra'ila, Netanyahu

  4. Tsohon ɗan wasan Man United Forlan zai fara buga gasar ATP Tennis

    Tsohon ɗan wasan Manchester United Diego Forlan zai fara wasansa na kwallon Tennis a matsayin kwararren ɗan wasan a wasan mutum biyu da za a yi a watan gobe a Uruguay.

    Mai shekara 45 ɗin, wanda ya yi murabus a 2019, zai buga wasan ne tare da takwaransa na Argentina Federico Coria a gasar Uruguay Open a Montevideo.

    Forlan wanda ke da sha'awar wasan Tennis tun yana yarinta, yana buga ITF Masters - ajin shekara 45 zuwa sama.

    Amma wasan da za a yi a watan gobe na ATP zai buƙaci Forlan ya mallakin katin manyan 'yan wasa masu buga gasa.

  5. Ramsey na son zama kocin Wales a nan gaba

    Aaron Ramsey ya bayyana burinsa na zama kocin Wales a nan gaba.

    Ramsey mai shekara 33, ya samu lasisin Uefa na zama koci, kuma yanzu haka yana matsayin koci kuma ɗan wasa a Cardiff City.

    Kyaftin ɗin Wales ɗin na da goyon bayan kocin ƙasar na yanzu Craig Bellamy, wanda yace yana da kwarin gwiwar idan Ramsey ya zama koci zai kai babban matsayi.

    Saboda bibiyar Bellamy sau da ƙafa a aikin da yake yi a matsayin kocin Wales, Ramsey ya tabbatar da cewa zai zama koci a nan gaba.

  6. La Liga na son Barcelona da Atletico Madrid su buga wasansu a Miami

    Hukumomin La Liga na son a buga wasan Barcelona da Atletico Madrid da aka tsara yi a watan Disamba a birnin Miami - amma idan Fifa ta amince.

    Wannan zai zama karon farko da za a buga wasan La Liga a Amurka.

    Hukumar kwallon ƙafa ta duniya Fifa ce za ta yanke hukunci na ƙarshe kan wannan buƙata.

    An tsara buga wasan ne a ranar 22 ga watan Disamba, gabanin La Liga su ta fi hutun lokacin sanyi.

  7. Ko tallafin da Wike zai bai wa ‘yan PDP a Sokoto na da alaƙa da takarar 2027?

    Yanzu za a iya cewa kallo ya fara komawa sama bayan rikicin cikin gida na jam'iyyar PDP ya ɗauki sabon salo a daidai lokacin da jam'iyyar ke ƙoƙarin shawo kan matsalolin da suka dabaibaye ta.

    A jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin ƙasar, wasu ƴaƴan jam’iyyar ne suka suka nuna goyon bayansu ga ministan Abuja Nyesom Wike, sakamakon shirinsa na tallafa musu da kuɗaɗe da kuma kayan abinci a ƙananan hukumomi 23 na jihar.

    "Wike ya neme mu a nan Sokoto domin mu yi tafiyarsa, sannan ya ce mu kira ƙungiyoyi a duk faɗin ƙananan hukumomi 23 domin ya riƙa tallafa musu kafin lokacin zaɓe," a cewar Ahmadi Abdullahi Oil and Gas shugaban ƴan PDP da suka nuna goyon baya ga Wike.

    "Wike ɗan PDP ne ko ɗan wata jam’iyyar daban? Ko a wane ɓangare yake idan dai a PDP ne za mu karɓe shi. Kuma tafiyar ta samu karɓuwa sosai," in ji shi.

  8. Rundunar haɗin gwiwar tsaro ta Iraƙi ta ce ta kashe shugaban IS

    Rundunar haɗin gwiwar tsaro ta Iraƙi ta ce dakarunta sun kashe shugaban ƙungiyar IS a ƙasar.

    A cikin sanarwar da suka fitar sun kira shugaban da Jassim al-Maz-ru Abu Abdul-ƙadir.

    Dakarun sun kuma ce sun kashe shi ne tare da wasu mambobin ƙungiyar takwas.

    Firai ministan Iraƙin, Mohammed Shi'a al-Sudani ya tabbatar da mutuwar kwamandan I-S din wanda ya ce an kashe shi a yayin wani samme da jami'an tsaro suka kai a tsaunukan Hamrin da ke arewa maso gabashin ƙasar.

  9. Matasan 'yanwasan Kano Pillars sun ji raunuka a hatsarin mota

    Tawagar 'yanwasan ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta yi hatsari a kan hanyarsu ta zuwa birnin Jos na jihar Filato.

    Ƙungiyar ta 'yan ƙasa da shekara 19 ta tafi Jos ne domin buga wasan mako na biyar da Plateau U-19 a gasar matasa.

    "'Yanwasa da yawa da kuma direban motar sun ji raunuka a hatsarin kuma nan take aka kai su asibiti," a cewar wani saƙo da ƙiungiyar ta wallafa a shafinta na X.

    Ta ƙara da cewa "cikin sa'a babu wanda ya rasu kuma tawagar likitoci na ci gaba da saka ido".

  10. Harin Isra'ila ya raunata ma'aikatan Red Cross uku a Lebanon

    Ƙungiyar ba da agaji ta Red Cross a Lebanon ta ce an kai wa ma'aikatan agajinta hari yayin da suke aikin ceto a Nabatieh da ke kudancin ƙasar.

    Cikin wani saƙo a dandalin X, Red Cross ta ce tana "ƙoƙarin zaƙulo waɗanda aka jikkata ne domin kulawa da su" sakamakon wani hari da aka kai da tsakar ranar yau.

    Ta ce sai da ta samu amincewar dakarun Majalisar Ɗinkin Duniya Unifl amma duk da haka aka kai wa inda suka je ɗin hari tare da "raunata ma'aikatan lafiya uku".

    Rundunar sojin Isra'ila ba ta ce komai ba game da lamarin, kuma da ma ba ta saba yin magana kan ɗaiɗaikun hare-hare ba.

  11. Labarai da dumi-dumi, An dakatar da majalisar dokokin Ghana sakamakon hatsaniya

    An dakatar da zaman majalisar dokokin Ghana bayan hatsaniyar da ta ɓarke tsakanin mambobin jam'iyya mai mulki da na adawa.

    An fara hayaniya ne bayan 'yanmajalisar adawa na jam'iyyar NDC sun samu rinjaye a safiyar yau Talata, abin da ya tilasta wa na jam'iyya mai mulki suka fice daga zaman.

    Lamarin ya ta'azzara ne sakamakon hukuncin kotun ƙolin ƙasar kan wasu 'yanmajalisa huɗu na adawa da suka bar jam'iyyarsu. Kotun ta yi watsi da matakin kakakin majalisar na ayyana kujerunsu a matsayin fanko.

    An ɓarke da hayaniya ne a zaman da ya kamata kakakin ya ayyana amincewa ko akasin haka da zamansu a majalisar, amma aka tashi ba tare da yanke wani hukunci ba.

  12. Blinken na tattaunawa da Netanyahu kan tsagaita wuta a Gaza

    Sakatren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken yana ganawa da Firaministan Isra'ila, kamar yadda ofishin shugaban ya bayyana.

    Wani hoto da aka wallafa a shafukan zumunta ya nuna mutanen na magana a cikin wani ofishi a Birnin Ƙudus.

    Balaguron na babban jami'in difilomasiyyar Amurka shi ne karo na 11 tun bayan fara yaƙin Gaza ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

    Wannan karon, ya je ne domin yunƙurin farfaɗo da tattaunawar tsagaita wuta a Gaza bayan kisan shugaban Hamas Yahya Sinwar, wanda Amurka da ƙasashen Yamma ke zargi da ƙin bai wa tattaunawar muhimmanci.

  13. Tangarɗa a layin lantarkin Ugwaji-Apir ce ta jawo rashin wuta a arewacin Najeriya - TCN

    Kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya TCN ya ce tangarɗa aka samu a layin lantarki na Ugwaji-Apir mai ƙarfin 330kV, wanda ya yi sanadiyar rashin wuta a arewacin ƙasar.

    Kamfanin ya ce matsalar ta shafi yankunan arewa maso gabas, da arewa maso yamma, da wasu ɓangarori na arewa ta tsakiya.

    Wata sanarwa da kamfanin na Transmission Company of Nigeria ya fitar ta ce: "Da misalin ƙarfe 4:53 na safiya ne layin lantarkin Ugwuaji-Makurɗi na biyu mai ƙarfin lantarki 330kV ya samu tangarɗa, sai aka tura lantarki mai ƙarfin megawat 243 zuwa layi na ɗaya a layin domin ci gaba da samar da wutar.

    "Sai shi ma da misalin ƙarfe 4:48 na safiyar ya samu matsala, wadda ta sa aka rasa lantarki mai yawan megawat 468. Da misalin ƙarfe 5:17, mun sake gwada layi na ɗaya da na biyun, amma dukkansu suka sake samun tangarɗa a tare."

    A makon da ya gabata ne babban layin lantarki na Najeriya ya lalace har sau uku cikin kwana biyu, abin da ya jefa duka ƙasar cikin duhu.

  14. Gwamnatin Kano ta dakatar da ƴanjarida 14 daga aiki a gidan gwamnati

    Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da ƴan-jarida 14 da ke aiki a fadar gwamnatin jihar daga aiki tare da neman sauyinsu daga hukumomin da suke ƙarƙashinsu.

    A wani saƙo da kakakin gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ga waɗanda abin ya shafa, ya umarce su da su koma wuraren aikinsu, tare da neman hukumominsu su aika da wasu da za su maye gurbinsu a gidan gwamnatin jihar.

    Babu wani dalili da kakakin ya bayyana na ɗaukar wannan mataki, illa dai ya buƙace su da su bi umarnin wanda ya fara aiki daga yau Talata.

    To amma a saƙon da ya rubuta a shafin WhatsApp na tawagar 'yanjaridar da ke aiki a fadar gwamnatin jihar ta Kano, Sanusin ya bayyana cewa : ''Abin takaici a lokacin da na yi tafiya zuwa ƙasar Serbia a makon da ya gabata, wasu abubuwa sun faru, saboda haka akwai buƙatar shugabancin a wannan mawuyacin hali ya ɗauki mataki...''

    Wasu daga cikin ƴanjaridar da abin ya shafa sun haɗa da na kafofin yaɗa labarai na gwamnatin jihar da na tarayya da kuma masu zaman kansu.

  15. Sakataren Wajen Amurka Blinken ya isa Isra'ila kan tsagaita wuta a Gaza

    Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken, ya sauƙa a Isra'ila don ƙoƙarin farfaɗo da yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta a Gaza da kuma tattaunawa kan sako mutanen da aka yi garkuwa da su.

    An shirya ziyarar ne, bayan kashe shugaban Hamas, Yahya Sinwar, da Isra'ila ta yi, inda gwamnatin Biden ta ga cewa dama ta samu ta farfaɗo da tattaunawar diflomasiyya.

    Sai dai Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana ƙarara cewa ba zai daina kai hare-hare ba har sai an murkushe Hamas.

    Mai yiwuwa Mista Blinken a yanzu zai mayar da hankali kan yadda za a mulki Gaza bayan rikicin, kuma ƙila zai matsa wa Isra'ila kan barin kayan agaji su shiga arewacin Zirin.

    Idan ya bar Isra'ila, Mista Blinken zai kuma nufi ƙasashen Larabawa a ci gaba da tattaunawar.

    Ziyarar ta Blinken ita ce ta 11 a Gabas ta Tsakiya tun bayan da aka fara yaƙin Gaza.

  16. Harin Isra'ila ya kashe mutum 13 da raunata 57 a kusa da asibiti a Lebanon

    Jami'an lafiya a Lebanon sun ce wani hari da Isra'ila ta kai ta sama a kusa da asibiti mafi girma na birnin ya kashe aƙalla mutum 13 tare da jikkata wasu 57, yawancinsu ƙananan yara.

    Sai dai sojojin Isra'ila sun ce sum kai harin na kudancin birnin Beirut ne, kan wani waje na ƙungiyar Hezbolah da ke kusa da asibitin kuma harin bai samu asibitin ba.

    To amma wakilin BBC a Beirut ya ce, harin duk da cewa ba a kaishi kai tsaye kan asibitin ba na Jami'ar Rafik Hariri ya yi illa sosai ga asibitin, wanda ya ce yanki ne da Hezbolla ke da ƙarfi.

    Isra'ilar ta kuma kai wasu hare-haren a kusa da babban filin jirgin saman Lebanon.

    Kungiyar Hezbollah dai ta ci gaba da harba rokoki zuwa arewacin Isra'ila, inda kuma Isra'ilar ta ce an tare yawancin makaman.

  17. Shugaba Putin zai nuna wa ƙasashen Yamma takunkuminsu ba ya aiki - Rasha

    A yau Talata ne Shugaba Putin na Rasha zai kasance mai masaukin baƙi ga tawagogi daga ƙasashe 36 waɗanda za su halarci taron ƙungiyar ƙasashen da arziƙinsu ke bunƙasa - BRICS.

    Fadar gawamnatin Rasha, Kremlin ta ce babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya ma zai halarci taron, kodayake mai magana da yawun Antonio Guterres ba bayar da tabbacin hakan ba.

    Daga cikin shugabannin da aka gayyata akwai, Xi Jinping na China, da Firaministan India Narendra Modi da shugaban Iran Masoud Pezeshkian.

    Moscow ta ce taron wata shaida ce da ke nuna cewa ƙoƙarin da ƙasashen yammacin Turai ke yi na mayar da Rasha saniyar-ware saboda mamayar da ta yi a Ukraine ya ci tura.

    Ana ganin fadar Kremlin za ta matsa lamba don ƙulla yarjejeniya kan sabon tsarin hada-hadar kuɗi tsakanin ƙasashen waɗanda babu ruwansa da dalar Amurka

  18. Kotu a Peru ta ɗaure tsohon shugaban ƙasar shekara 20 saboda rashawa

    Wata kotu a Peru ta yanke wa tsohon shugaban ƙasar Alejandro Toledo hukuncin ɗaurin shekara ashirin da wata shida a gidan yari bisa samunsa da laifin almundahana da halasta kuɗaɗen haram.

    Masu gabatar da ƙara sun ce ya karɓi fiye da dala miliyan 30 a matsayin cin hanci daga wani kamfanin gine-gine na Brazil wanda aka ba shi kwangilar gina titi a kudancin Peru.

    Babban mai gabatar da kara na ƙasar ta Peru, Jose Domingo Perez, ya ce, wannan hukunci ne mai cike da tarihi, inda ya ƙara da cewa sako ne na cewa babu wanda ya fi ƙarfin doka a ƙasar.

    Mista Toledo mai shekara 77 ya yi mulki ne daga shekarar 2001 zuwa 2006.

  19. MDD ta buƙaci Indonesia ta kuɓutar da Musulmi ƴan Rohingya daga teku

    Hukumar kula da ƴan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi kira ga gwamnatin Indonesia da ta kuɓutar da wani jirgin ruwa da ke cike da ƴan gudun hijirar Rohingya fiye da 100.

    Jirgin ya kafe ne a gabar tekun lardin Aceh da ke yammacin Indonesia ɗauke da mutanen waɗanda Musulmi ne.

    A makon da ya gabata an kai biyar daga cikin ƴan gudun hijiran zuwa asibiti a Indonesia.

    Ana ci gaba da tattaunawa tsakanin Majalisar Ɗinkin Duniya da gwamnatin ƙasar KAN LAMARIN.

    A kowace shekara, dubban ƴan kabilar Rohingya suna tserewa daga Myanmar inda ake muzguna musu.

  20. Mutum ɗaya ya rasu, 15 sun jikkata bayan jiragen ƙasa biyu sun yi taho-mu-gama a Wales

    Mutum ɗaya ya rasu bayan jiragen ƙasa biyu sun yi taho-mu-gama a Wales, kamar yadda ƴansandan kula da sufuri na Burtaniya (BTP) suka bayyana.

    Haka kuma mutum 15 sun jikkata a sanadiyar hatsarin wanda ya auku a kusa da garin Llanbrynmair tsakanin jirgin da ya taso daga Shrewsbury zuwa Aberystwyth da wanda ya taso daga Machynlleth zai tafi Shrewsbury.

    Wani fasinja da ke cikin jirgin da zai tafi Shrewsbury ya ce lamarin ya haifar da tashin hankali sosai.