Lebanon ta ce wani harin jirgi maras matuƙi da Isra'ila ta kai ƙasar ya kashe mutum biyu
Ma'aikatar lafiya a Lebanon ta ce mutum biyu sun mutu bayan harin da Isra'ila ta kai da jirgi maras matuƙi a kudancin ƙasar.
Mutanen biyu dai na tuka keke a lokacin da harin ya faɗa kansu a kusa da garin Taybeh.
Sojin Isra'ila sun ce jirgin yaƙinsu sun kai hari wasu gine-gine da sukai amanna mayaƙan ƙungiyar Hezbollah da Iran ke mara wa baya na amfani da su a ƙauyen Odaisseh, kusa da iyakar ƙasashen biyu.
Shugaban ƙungiyar Hezbollah, Hassan Nasrullah ya maida martani da cewa maƙiyan ƙungiyarsa su dakaci martanin da ya kira 'mai tsair' da za su mayar.
Ya ƙara da cewa duk wanda ya taɓa ƙungiyar to ba za su ƙyale shi ba.
Ƙungiyar Hezbollah da sojin Isra'ila, na kai wa juna hari tun bayan kisan kwamandansu da jagoran siyasar Hamas Isma'il Hanniyeh.