Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/08/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/08/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi da Aisha Babangida

  1. Ƙungiyar likitoci ta zargi RSF da kisan kiyashi a El Fasher ta Sudan

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Ƙungiyar likitoci a Sudan ta zargi mayaƙan RSF da aikata kisan kiyashi akan fararen hula a yayin da suke ci gaba da lugudan wuta a El Fasher, ɗaya daga cikin biranen dake Darfur wanda kuma basa iko da shi.

    Ƙungiyar ta ce mutane 24 sun mutu a wani hari da suka kai tsakiyar wata kasuwa da ke yankin.

    Babu wani tabbaci a hukumance a game da hakan, to amma ana yawan zargin mayaƙan na RSF da zafafan hare-hare a yayin da suke ƙarfafa kawanyar da suka yi wa yankin.

    Fiye da shekara guda kenan mayaƙan RSF na yi wa El Fasher kawanya kuma a tsawon wannan lokaci mayaƙan na aikata laifukan yaƙi sosai a yankin.

    A ƙarshen makonnan an kashe wasu mata da yara a yayin da suke ƙoƙarin barin birnin.

  2. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a hantsin Juma'a.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassa na duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.