Gobara ta kashe mutum 11 a cibiyar kula da yara ta Aljeriya

Asalin hoton, Algeria's General Directorate for Civil Protection
Mutum 11 ne suka mutu sakamakon wata gobara da ta tashi a wata cibiyar kula da yara da ke Algiers, babban birnin ƙasar Aljeriya.
Hukumar kare fararen ta ƙasar ta ce gobarar, wadda ta tashi da tsakar dare, ta kuma raunata mutum 19.
Jami'an hukumar sun ce har yanzu suna aiki domin kammala daƙile wutar.
Zuwa yanzu hukumar ba ta bayyana maƙasudin tashin gobarar ba.
Aljeriya ta kwashe kwanaki tana fama da tsanann zafin rana, yayin da kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayar da rahoton samun gobara fiye da 1,000 a ƙasar cikin mako guda.
Hukumar kare muhalli ta ƙasar ta ce an samu rahotonnin gobarar daji 115 a cikin kwana guda.
Shugaban ƙasar, Abdelmadjid Tebboune ya aike da saƙon jaje ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa a cibiyar kula da ƙananan yaran, bayan mai bayyana lamarin da ''babban rashi''.
























