Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/11/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/11/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi, Abdullahi Bello Diginza, Isiyaku Muhammed da Ahmad Bawage

  1. China ta tura ɗanjarida gidan yari bisa zargin leƙen asiri

    China

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Dong Yuyu ne ɗanjaridan da aka tura gidan yari

    Wata kotu ta yanke wa wani ɗanjarida a ƙasar China hukuncin zaman gidan kaso na shekara bakwai bisa zarginsa da leƙen asiri, kamar yadda iyalansa suka shaida wa BBC.

    Dong Yuyu, mai shekara 62, ya kasance a tsare tun a shekarar 2022, kuma ya kasance fitaccen ɗanjarida a ƙasashen Amurka da Japan, kuma yana yawan ganawa da jakadun ƙasashen waje.

    Ƴansanda sun kama shi ne a daidai lokacin da yake ganawa da jakadan ƙasar Japan a birnin Beijing.

    Dong na cikin manyan ƴanjarida na kafar Guangming Daily, wadda take ɗaya daga cikin manyan jaridu guda biyar da suke da alaƙa da jam'iyyar gurguzu ta China.

    Iyalansa sun bayyana a wata sanarwa cewa, kotun ta ce ma'aikatan ofishin jakadancin Japan da Dong ya gana da su "ƴan leƙen asiri ne.

    "Muna mamakin yadda gwamnatin China za ta kira ofishin jakadanci 'masu leƙen asiri," kamar yadda sanarwar iyalan ta nuna.

  2. Za mu cigaba da yaƙi idan Hezbollah ta saɓa yarjejeniya - Netanyahu

    Netanyahu

    Asalin hoton, Reuters

    Firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya sake nanata cewa sojinsa za su cigaba da yaƙi da Hezbollah matuƙar ƴan ƙungiyar suka saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma tsakaninsu.

    A wata hira ta kafar talbijin, ya ƙi bayyana yarjejeniyar da Amurka ta shiga tsakani a matsayin ta kawo ƙarshen yaƙin. Ana ci gaba da amfani da yarjejeniyar duk da yake Isra’ila ta kai hare-hare ta sama da ta ƙasa duk da fara aikin yarjejeniayr a farkon makon nan.

    Sojojin Lebanon sun zargi Isra’ila da karya sharuɗɗan yarjejeniyar.

    Yayin da ita ma ƙungiyar Hezbollah ta ce an kai wa ƙauyukan da ke iyakar ƙasasshen biyu hari, lokacin da mutane ke ƙoƙarin komawa muhallansu.

  3. Gwamnatin Kaduna ta sake buɗe kasuwar Birnin Gwari bayan kusan shekara 10 a rufe

    Uba Sani

    Asalin hoton, OTHER

    Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya sake buɗe kasuwar Birnin Gwari bayan kusan shekara goma tana rufe, sannan ya karɓi wasu tubabbun ƴanbindiga da suka ajiye makami suka rungumi zaman lafiya.

    Ya ce gwamnatin jihar Kaduna tare da haɗin gwiwar wasu ɓangarorin gwamnatin tarayya, ta kafa kwamitin wanzar da zaman lafiya ta hanyar tattaunawa, domin samar da zaman lafiya mai ɗaurewa.

    "Ta hanyar tattaunawa, yanzu mun samu amincewar mutanenmu. Yanzu manyan jagororin ƴanbindiga da dama sun miƙa wuya tare da yaransu," in ji shi, kamar yadda shafin intanet na tashar Chanells ya ruwaito.

    Ya ƙara da cewa waɗanda suka miƙa wuya, ana sanya su a shiri na musamman na gyara tunani domin tabbatar da cewa sun koma cikin al'umma sun cigaba da rayuwarsu yadda ya kamata.

    Sai dai ya ce waɗanda suka ƙi miƙa wuya kuma, "ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar mataki a kan su. Tuni jami'an tsaro sun fara samun nasara a kan ƴanbindigar tare da ceto wasu waɗanda aka yi garkuwa da su," in ji shi.

  4. Nukiliya: Iran ta faɗaɗa ayyukan tace makamashin uraniun - Rahoto

    Iran

    Asalin hoton, Reuters

    Wani rahoton sirri na hukumar da ke sa ido kan makaman nukiliya ta MDD ya ce Iran ta sanar da su shirinta na samar da na'urar tace makamashin uranium da take samarwa.

    Rahoton na IAEA da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani, ya nuna Iran na shirin samar da na'urar sama da 5000 a cibiyoyi biyu da take da su a ƙasar.

    Wannan na zuwa ne bayan manyan mambobin IAEA sun amince da wani ƙuduri a makon da ya wuce, na ƙin amincewa da matakan faɗaɗa makaman nukiliyar da Iran ke yi.

    Nan gaba a yau ake sa ran Iran za ta tattauna da Burtaniya da Faransa da Jamus a Geneva, kan shirin ta na makamin nukiliya.

  5. Ƙasar Chadi ta yanke alaƙar soji tsakaninta da Faransa

    Shugaban ƙasar Chadi

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Matakin na zuwa ne sa'o'i bayan ganawar shugaban Chadi da ministan harkokin wajen Faransa

    Gwamnatin ƙasar Chadi ta ce ta yanke huldar ayyukan soji tsakaninta da Faransa.

    A cikin wata sanarwa da ya fitar a daren ranar alhamis, ministan harkokin wajen ƙasar Abderaman Koulamallah ya ce "an dauki matakin ne bayan nazari mai zurfi," yana mai cewa matakin ''wani sauyi ne a tarihin ƙasar''.

    Sanarwar ta zo ne sa'o'i kaɗan bayan ziyarar Ministan harkokin wajen Faransa, Jean-Noel Barrot wanda ya gana da shugaban ƙasar Chadi Mahamat Deby a safiyar ranar Alhamis.

    Ƙasar Chadi ta kasance babbar aminiya ga ƙasashen yamma, ta fuskar yaƙi da masu ikirarin jihadi a yankin Sahel.

    Kawo yanzu dai ba a san dalilin da ya sa ƙasar ta kawo ƙarshen yarjejeniyar - wadda aka yi wa kwaskwarima a shekarar 2019.

    Mista Koulamallah ya ce "Lokaci ya yi da ƙasar Chadi za ta tabbatar da cikakken ikonta, kuma ta sake fayyace dangantaka da abokan hulɗarta," shekaru 66 bayan ayyana 'yancin kai.

  6. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa -kai tseye barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'a, Haji babbar rana kamar yadda Hausawa ke yi mata kirari.

    Sannunku da sake kasancewa da mu a daidai wannan lokaci da za mu leƙe lungu da saƙo na duniya domin kawo muku labaran da ke faruwa.

    Kuna iya kasancewa da mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawar.