El-Rufai ya sake gurfana a kotun Kaduna bayan makokin mahaifiyarsa

Asalin hoton, Mal. Imran U.Wakili (PULLO)/X
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya sake gurfana a gaban Babbar Kotun Jihar Kaduna a ranar Talata kan tuhume-tuhume da hukumar yaki da cin hanci da rashawa (ICPC) ta shigar a kansa.
An gurfanar da El-rufai ne kan zargin laifuka da suka haɗa da amfani da muƙami ba bisa ƙa’ida ba, damfara, da bai wa wasu dama fiye da yadda ya dace, da kuma wasu tuhume-tuhume da suka shafi kudade.
El-Rufai ya bayyana a kotun ne bayan ICPC ta sake shi daga tsare shin da tayi na fiye wata guda, wanda hakan ya biyo bayan rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Ummar El-Rufai, a Cairo, Masar..
Bayan kammala gurfanar da shi babbar kotun jihar, za a kai El-Rufai Kotun Tarayya da ke Kaduna, inda za a fara sauraron buƙatar belinsa da ya shigar.
Ana sa ran cewa za a duba batun belinsa cikin gaggawa, saboda irin nauyin tuhumomin da ake masa.




