'Jirgin sojojin Najeriya ya kashe ƴan fashin daji sama da 80 a Katsina'

Asalin hoton, fb/Nigerian Airforce
Rundunar sojin Najeriya ta sanar da cewa ta kashe sama da ƴan bindiga 80 tare da ƙona babura 45 waɗanda ƴan fashin ke amfani da su a jihar Katsina.
Wata sanarwa da rundunar sojin sama ta Najeriya ta fitar a yau Litinin, wadda ta samu sa hannun daraktan hulɗa da jama'a da yaɗa labarunta, Edward Gabkwet, ta ce an kai harin ne a wata maɓuyar ƴan bindiga da ke ƙauyen Gidan Kare a ƙaramar hukumar Faskari da ke jihar ta Katsina.
Katsina na cikin jihohin Najeriya da ke fuskantar matsalar ƴan fashin daji masu kisa da garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa.
Sanarwa sojojin ta ce ta kai harin ne ranar Asabar a lokacin da ta samu rahoton cewa ƴan bindiga kimanin 100 sun kai hari a wani ƙauyen da ke da nisan kilomita biyar daga Gidan Kare, inda suka riƙa ƙona gidajen al'umma.
Ta ƙara da cewa da misalin ƙarfe 9:40 na daren ranar ne jirgin rundunar ya yi ruwan wuta a kan ƴan fashin dajin waɗanda suka taru a kusa da dabar Kuka Shidda, inda bayanai suka tabbatar da cewa an kashe sama da ƴan bindiga 80 da ƙona babura 45.

Asalin hoton, Nigerian Airfoce
Haka nan sanarwar ta ce an gano cewa ƴan fashin da aka kashen suna da alaƙa ne da "gawurtattun ƴan bindiga Yusuf Yellow da Rabe Imani".
A watan Oktoban 2023 ne gwamnatin jihar Katsina ta kafa ƙungiyar ƴan sintiri waɗanda ta ce za su taimaka mata a yaƙin da take yi da ƴan fashin daji, waɗanda suka tagayyara al'umma a ƙauyuka tare da hana gudanar da ayyukan noma.
Cikin tattaunawarsa da BBC a baya-bayan nan, gwamnan jihar, Dikko Radda ya ce a yanzu "matsalar ƴan fashin daji ta taƙaita ne ga wasu ƙananan hukumomi guda takwas" a cikin 37 na jihar.
Kuma ya bayyana cewa gwamnati na yin bakin ƙoƙarinta wajen shawo kan lamarin.














