Dalilin da ya sa aka saki fursunoni 888 a Najeriya

Asalin hoton, Google
Hukumi a Najeriya sun ce an saki mutum 888 da aka zarga da alaƙa da ta'addanci saboda gaza samun isassun hujjoji a kansu da kotu ta yi.
Gwamnatin Najeriya ta ce daga 2017 an gabatar da mutum 1,743 daga lokaci na farko zuwa lokaci na shida na sauraren shari'ar da ake yi wa waɗanda ake zargi da ta'addanci da ake tsare da su a gidan yarin Kainji.
Daraktan gabatar da ƙara na tarayya Mohammed Abubakar Babadoko ne ya bayyana hakan ga manema labarai a yau a Abuja.
"An yanke wa mutum 742 hukuncin a duka tsawon wannan lokacin - yayin da aka ɗage sauraren ƙarar 92 daga cikin waɗanda ake tuhuma.
"Idan na ɗauki abin daki-daki a watan Oktobar 2017, an yankewa mutum 50 hukunci an saki 203 yayin da aka ɗage sauraren ƙarar 28.
"A watan Fabirairun 2018 an yankewa 203 hukunci aka saki 582 sannan aka ɗage sauraren ƙarar mutum 24.
"A watan Yulin shekarar dai an yankewa 113 hukunci sannan 102 aka sake su - aka ɗage sauraren ƙarar 9.
"A watan Disambar 2023 an saki mutum ɗaya da aka samu ba laifi sannan kuma an yanke wa 14 hukunci aka ɗage sauraren ƙarar 10.
"A 2024 da muke ciki a watan Yuli an yankewa 125 hukuncin yayin da aka ɗage sauraren ƙarar 21. A dai shekar an yanke wa mutum 237 hukunci".
Da haka adadin ya kai yadda aka bayyana a jumlace tun da fari.


















