Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 15/05/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 15 ga watan Mayun, 2024.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza and Umar Mikail

  1. Za mu kafa kwamiti don binciken yadda aka mulki Rivers - Fubara

    ..

    Asalin hoton, X/Siminalayi Fubara

    Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce zai kafa kwamiti domin gudanar da bincike kan gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike.

    A baya-bayan nan dai danganta ta yi tsami tsakanin ɓangarorin biyu, har ma gwamna Fubara ya zargi Wike da bar wa jihar tarin bashi.

    A cikin wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta an ga gwamna Fubara na cewa ''Duk wanda ya ɗauki bindiga da nufin kisa, to in ka samu dama kai ka binne shi''.

    ''Za mu buɗe sabon babi a jihar Rivers, shiru-shiru ba tsoro ba ne, gudun fitina ne, a baya na yi shiru ne saboda mun fito daga gida guda, amma a yadda yake a yanzu, masu iya magana na cewa ɗan zaki ya girma'', in ji Fubara.

    Ya ce ''Za mu kafa kwamitin bincike, domin gudanar da bincike kan lamuran gwamnati, kuma ba zan janye wannan mataki ba''.

    ''Dole ne mu ci gaba, kuma in dai ci gaba na nufin ɗaukar matakan da ba za su yi wa wasu daɗi ba, to lallai su shirya domin kuwa ba gudu ba ja da baya'', in ji gwamnan

    ''Watakila wasu na gaya musu cewa ba abin da zai faru ne,amma tabbas su sani cewa lallai wani abu zai faru, kuma Allah yana tare da mu, ba za mu bari wani ya yaudare mu ba''.

    Da alama gwamnan na jawabi ne a wani taro, domin kuwa a cikin bidiyon ana jiyo muryar wasu na yaba wa gwamnan a yayin da yake gabatar da jawabin.

  2. Dakarun yaƙi da ta'addanci a tafkin Chadi sun ƙaddamar da jerin samame

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin haɗin gwiwa mai yaƙi da ayyukan ta'addanci a yankin tafkin Chadi ta ƙaddamar da jerin samame cikin ƙasashen yankin, inda suka kashe ɗan bindiga guda tare da kwace makamai da kayayyaki.

    Cikin wata sanarwa da jami'ain hulda da jama'a ana rundunar Laftanar kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce a ranar 13 ga watan Mayu sojojin rundunar sun kai samame tsibirin Litri da ke kan iyakar Najeriya da Chadi, inda suka kashe ɗan bindiga guda, tare da ƙwato bindiga guda ƙirar AK 47 da kwanson zuba harsasai guda biyu,da na'urar tara da abin fashewa

    Haka kuma sanarwar ta ce a ranar 11 ga watan na Mayu dakarun rundunar sun ka wani samamen kan mayaƙan Boko Haram a garin Burwarti da ke yankin ƙaramar hukumar Kukawa a jihar Borno da ke Najeriya.

    ''Samamen ya haddasa ƙwace babura biyu da buhun gero huɗu da sauran kayyaki'', in ji sanarwar.

    Rundunar haɗin gwiwar ta kuma ce a ranar 13 ga watan Mayu, dakarunta da ke Nijar sun ƙwace man fetur da aka ɓoye cikin buhunan masara a jihar Diffa.

    Wannan yunƙuri na dakarun ya daƙile yunƙurin fasa ƙwaurin man da 'yan bindigar ke yi a yankin tafkin Chadi.

  3. Hamɓararren shugaban Gabon ya fara yajin cin abinci

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Hamɓararren shugaban ƙasar Gabon, Ali Bongo tare da 'ya'yansa biyu sun fara yajin cin abinci domin nuna adawa kan abin da suka kira ''Cutarwa da zalincin'' da ake yi musu, kamar yadda lauyoyinsu suka bayyana.

    A watan Agustan da ya gabata ne sojoji suka kifar da gwamnatin mista Bongo, jim kaɗan bayan lashe zaɓn shugaban ƙasar da ke cike da zargin maguɗi.

    Daga nan ne kuma sojojin ke ci gaba da tsare da shi a gidansa da ke Libreville, babban birnin ƙasar tare da 'ya'yansa biyu, Jalil and Bilal.

    Sojojin mulkin ƙasar sun kuma kai matarsa Sylvia Bongo da babban ɗansa Noureddin gidan yari, inda suke zaman jiran shari'a kan zarge-zargen rashawa.

    Cikin sanarwar da lauyoyinsu suka fitar, sun yi zargin cewa ana dukan Noureddin da Sylvia tare da azabtar da su a lokacin da ake tsare da su.

    Sun kuma yi zargin cewa ana azabtar da Noureddin ta hanyar jona masa ''wayoyin lantarki''.

    Kawo yanzu dai hukumomin ƙasar ba su ce komai ba game da zarge-zargen.

    Ali Bongo ya jagoranci ƙasar mai arzikin man fetur tun 2009 lokacin da ya gaji mahaifinsa, wanda ya shafe shekara fiye da 40 a kan karagar mulki.

  4. A yau za a fara jigilar maniyyatan Najeriya zuwa Saudiyya

    ..

    Asalin hoton, NAHCON

    A yau ne hukumar Alhazan Najeriya za ta fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa ƙasa mai tsarki domin sauke farali.

    Za a ƙaddamar da fara jigilar maniyyatan bana ne a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin ƙasar.

    Tuni shugaban hukumar Alhazan ƙasar, Jalal Ahmed Arabi tare da wasu jamai'an hukumar suka isa jihar, domin duba shirye-shiyen da hukumar ta yi gabanin fara jigilar maniyyatan.

    Nahcon ta ce jirgin farko da zai tashi daga filin jirgin saman, Sir Ahmadu Bello da ke Birnin Kebbi, zai ɗauki maniyyata 428.

    ''Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ne zai kasance babban baƙo a wajen bikin ƙaddamarwar,'' kamar yadda Nahcon ɗin ta wallafa a shafinta na Facebook.

    Nahcon ta kuma ce tun a ranar Lahadi ne hukumar Alhazan ta ce tawagar jami'an lafiya da manema labarai da masu kula da masaukai da kwamitin ciyarwa da sauran kwamitoci suka tashi zuwa ƙasa mai tsarkin domin shirya fara shirye-shirye.

    Hukumar alhazan ta ce za a ci gaba da jigilar alhazan har zuwa ranar 10 ga watan Yuni.

    Nahcon ta ce an zaɓi filayen jiragen sama 15 domin gudanar da jigilar maniyyatan na bana.

    Kusan maniyyatan Najeriya 65,047 ne ake sa ran za su sauke farali a bana kamar yadda hukumar ta bayyana.

    ..

    Asalin hoton, NAHCON

    Bayanan hoto, Tawagar jami'an lafiya da kwamitin kula da masaukai da hukumar Alhazan Najeriya ta tura Saudiyya
  5. Alaƙarmu da China ta inganta fiye da yadda ake tsammani - Putin

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Vladimir Putin na Rasha da shugaban China, Xi Jinping

    Shugaban Rasha Vladimir Putin ya ce alaƙa tsakanin Rasha da China ta inganta sama da yadda ake tunani.

    Mista Putin na waɗannan kalamai ne a jajibirin ziyarar da ya kai birnin Beijing.

    A wata tattaunawa da kafar yada labaran China, shugaban na Rasha ya jinjina wa ƙasashen biyu kan alaƙarsu da kuma yaba wa China da har cikin zuciya take son ganin an kawo ƙarshen yaƙin Ukraine, a cewarsa.

    Ziyarar mista Putin zuwa China da kuma gana wa da 'yan jarida alamomi ne da ke nuna zai zai yi ƙoƙarin shawo kan China ta cigaba da mara masa baya wajen cimma burinsa na mamayar Ukraine da kuma taimaka wa harkokin kasuwancinsu da ƙasashe suka ƙauracewa

  6. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba da Hausawa ke yi wa kirari da ta Bawa ranar samu.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci, domin kawo muku halin da duniya ke ciki, za mu mayar da hankali kan Najeriya da makwabtanta.

    Kar ku manta manya kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.