Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Usman Minjibir and Abdullahi Bello Diginza

  1. Ana bincike kan haɗarin jirgin da ya halaka babban jami'in sojin Kenya

    Gwamnatin Kenya ta tura wata tawaga domin gudanar da bincike kan hadarin jirgin helikwafta da ya kashe babban jami'in rundunar sojin ƙasar Janar Francis Ogolla da wasu tara.

    Zuwa yanzu ba a san abin da ya janyo hadarin jirgin ba.

    Janar Ogolla na cikin fasinjoji 12 da ke cikin jirgin sojin da ya gamu da haɗari ranar Alhamis jim kadan bayan ya tashi a arewa maso yammacin ƙasar.

    An miƙa gawarwakin mutanen da suka mutu zuwa Nairobi sannan mutum biyu da suka tsira na samun kulawa a asibiti.

    Da yake sanar da ayyana makokin kwana uku, shugaba William Ruto ya ce mutuwar mutanen ta jefa al'ummar ƙasar cikin baƙin ciki da jimami.

  2. Abin da muka sani game da harin Isra'ila a Iran

    An bayar da rahoton wani makami mai linzami na Isra'ila ya faɗa Iran, kusan mako ɗaya bayan da Iran ɗin ta kai wani harin ba-zata kan Isra'ila a ƙarshen makon da ya gabata.

    Ga abin da muka sani zuwa yanzu game da harin:

    • Wani makami mai linzami na Isra'ila ya kai hari kan Iran, jami'an gwamnatin Amurka sun faɗa wa kafar yaɗa labarai ta CBS inda aka ji ƙarar fashe-fashe a Isfahan da safiyar Juma'a, in ji rahotanni daga kafafen yada labaran Iran.
    • Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce an lalata jirage marasa matuƙi uku bayan da aka kunna shirin daƙile harin makami mai linzami.
    • Sun ruwaito wani janar ɗin soji a lardin Isfahan na cewa harin bai janyo ɓarna ba.
    • Lardin Isfahan gida ne ga babban sansanin jiragen soji da babbar cibiyar ƙera makamai masu linzami da cibiyoyin nukiliya da dama. Hukumar nukiliya ta duniya IAEA ta ce ba babu cibiyoyin nukiliya da aka lalata.
    • Ma'aikatar tsaron Amurka Pentagon da rundunar sojin Isra'ila ba su ce komai ba zuwa yanzu.

    Waiwaye:

    • Iran ta kasance cikin shirin ko-ta-kwana bayan da Isra'ila ta ce za ta mayar da martani ga harin da Iran ta kai mata ranar Asabar da daddare
    • Iran ta ƙaddamar da hare-hare na makamai masu linzami 300 da jirage marasa matuƙa kan Isra'ila ranar 13 ga watan Afrilu a wani harin ba-zata. Isra'ila da ƙawayenta na ƙasashen yamma sun daƙile akasarin hare-haren kafin su kai ga yankin Isra'ila
    • Iran ta dage cewa harin martani ne ga harin da ake zargin Isra'ila ta kai wa ofishin jakadancinta da ke Syria abin da ya halaka mutum 13.
    • Isra'ila ta nuna cewa za ta yi martani sai dai shugabannin ƙasashen duniya suna ta kira a gare ta da ta kai zuciya nesa
    • Kafafen yaɗa labaran Amurka da dama sun ruwaito cewa Amurka ta samu sanarwa ta masaniya game da hare-haren na Isra'ila
  3. Ɗan Najeriya na neman kafa tarihi a wasan dara

    Wani ɗan Najeriya da ya ƙware a wasan dara, Tunde Onakoya na ƙoƙarin kafa tarihi na nuna bajinta a wasan dara.

    Ya ƙuduri aniyar shafe sa'a 58 yana wasan tare kuma da amfani da damar wajen tara dala miliyan ɗaya da zai bayar ga mabuƙata.

    Kuɗin, a cewarsa, zai taimaka wa ilimin wasan dara ga miliyoyin yara.

    Ɗaruruwan magoya baya sun yi dafifi a dandalin Times Square da ke New York a Amurka domin nuna masa goyon baya ciki har da fitaccen mawaƙin Najeriya, Davido.

    Ƴan Najeriya da ke New York sun kasance tare da Onakoya inda suke ƙara masa ƙwarin gwiwa ta hanyar saka kiɗe-kiɗe da kuma rarraba abincin gargajiya na Najeriya har da shinkafa dafa-duka.

    A Najeriya ma, mutane na nuna goyon bayansu ga Onakoya yayin da suke kallon yadda yake nuna bajinta a ƙoƙarin kafa tarihi ta manhajar Twitch.

    Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya wallafa saƙon goyon baya ga Mista Onakoya a shafinsa na intanet inda ya ƙara ƙarfafa masa gwiwa da neman ya ƙara fito da Najeriya a idon duniya.

    Shi ma gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya faɗa wa Onakoya cewa yunƙurin da yake "babbar manuniya ce cewa ɗaukaka na iya zuwa daga ko ina."

    Zuwa ƙarfe 3:00 agogon New York ne Mista Onakoya ya shafe sa'a 39 yana wasan na dara kuma ya tara fiye da dala dubu 42.

    Waɗanda ke riƙe da kambun, Hallvard Haug Flatebo da Sjur y Ferkinstad sun shafe sa'a 56 da minti tara da sakanni 37 suna wasan dara a 2018.

    • Me ya sa ƴan Najeriya ke rige-rigen shiga Kundin Bajinta na Guiness?
  4. Kenya na makokin mutuwar babban jami'in sojinta a haɗarin jirgi

    Ana zaman makoki na kwanaki uku a ƙasar Kenya don jimamin mutuwar babban hafsan hafsoshin tsaron kasar (CDF) Janar Francis Omondi Ogolla wanda ya mutu a wani jirgin sama da ya yi hatsari a lardin Elgeyo Marakwet da ke arewa maso yammacin kasar.

    Ogolla, mai shekaru 61, ya mutu ne ranar Alhamis tare da wasu jami’an soji 9 da suka yi masa rakiya zuwa wani aiki na tantance yanayin tsaro a yankunan arewa maso yammacin Kenya da ke fama da matsalar rashin tsaro.

    A wani jawabi da ya yi wa al'ummar kasar sa'o'i bayan hatsarin jirgin, shugaba William Ruto ya ce Kenya ta yi asarar "ɗaya daga cikin manyan hafsoshinta".

    Tsohon shugaban ƙasar Uhuru Kenyatta da jagoran 'yan adawa Raila Odinga da jakadiyar Amurka Meg Whitman na daga cikin jagororin da suka yi ta'aziyyar mutuwar babban jami'in sojin na Kenya.

    Marigayi Janar ɗin ya shiga rundunar sojojin Kenya (KDF) a shekara ta 1984 kuma ya kai matsayin babban kwamandan sojojin ƙasar a bara.

    • Yadda mata ke zuwa asibitocin bayan fage don zubar da ciki a Kenya
  5. Al'ummar Indiya na kaɗa ƙuri'a a babban zaɓen ƙasar

    Al'ummar Indiya sun fara kaɗa kuri'a a zaɓen da aka kasa gida bakwai cikin makonni shida, inda kusan mutane biliyan ɗaya suka cancanci kaɗa ƙuri'a.

    Jam'iyyar BJP mai mulki ƙarƙashin jagorancin Firaiminista Narendra Modi, ta kasance a kan karagar mulki tun shekara ta 2014. A yanzu kuma tana neman ƙarin wa'adi.

    Yayin yaƙin neman zaɓe BJP na mayar da hankali kan ƙidar kishin addinin Hindu da ci gaban tattalin arziki da kuma inganta rayuwar al'umma.

    Ita kuwa babbar abokiyar hamayyarta Jam'iyyar Congress ta ƙulla ƙawance da ɗimbin jam'iyyun siyasar yankin don ƙoƙarin daƙile farin jinin Mista Modi.

    Ana sa ran sakamako a ranar 4 ga watan Yuni.

    • Ko Indiya ka iya zama babbar ƙasa me faɗa-a-ji a duniya?
  6. Barka da Juma'a

    Masu bibiyar mu barkan ku da warhaka. Barka da sake kasance da ku a shafinmu da muke kawo muku bayanan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya.

    Da fatan za ku kasance da mu a wanna rana domin ci gaba da kawo muku bayanai kai tsaye.