Jiragen yaƙin Turkiyya sun 'kashe farar hula 18' a kudancin Somaliya
Mayakan Al-Shabab na Somaliya sun yi iƙirarin cewa jiragen saman Turkiyya marasa matuka sun kashe fararen hula 18 a wani masallaci a ƙauyen Bagadaza kusa da kudancin garin Afgoye a yankin Shabeele a daren jiya.
Gidan rediyon Andalus mai magana da yawun al-Shabab ya ruwaito a yau cewa waɗanda suka mutu a harin da jirgin mara matuki ya kai sun haɗa da yara bakwai da mata shida.
“Jiragen marasa matuka mallakin gwamnatin Turkiyya sun fara harba makami mai linzami a wani masallaci a ƙauyen Bagadaza, inda mutane ke sallar Taraweeh (sallar dare ta musamman da aka yi a cikin watan Ramadan).
Bayan haka, waɗanda suka tsira daga harin na ƙokarin tserewa zuwa ƙauyen ne aka sake harbo su da makami mai linzami na biyu,” in ji Rediyon Andalus.
Al-Shabab ta ƙara da cewa mutane 12 kuma sun jikkata a harin da aka kai ta sama.
Kawo yanzu dai babu wani tabbaci kan wannan ƙazamin harin da ake zargin an kai.
- Abubuwan da ba ku sani ba game da ƙasar Somaliya
- Yadda ƴan Somaliya ke amfani da manhajar koyon karatu



