Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Nabeela Mukhtar Uba, A'isha Babangida, Haruna Kakangi and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Jiragen yaƙin Turkiyya sun 'kashe farar hula 18' a kudancin Somaliya

    Mayakan Al-Shabab na Somaliya sun yi iƙirarin cewa jiragen saman Turkiyya marasa matuka sun kashe fararen hula 18 a wani masallaci a ƙauyen Bagadaza kusa da kudancin garin Afgoye a yankin Shabeele a daren jiya.

    Gidan rediyon Andalus mai magana da yawun al-Shabab ya ruwaito a yau cewa waɗanda suka mutu a harin da jirgin mara matuki ya kai sun haɗa da yara bakwai da mata shida.

    “Jiragen marasa matuka mallakin gwamnatin Turkiyya sun fara harba makami mai linzami a wani masallaci a ƙauyen Bagadaza, inda mutane ke sallar Taraweeh (sallar dare ta musamman da aka yi a cikin watan Ramadan).

    Bayan haka, waɗanda suka tsira daga harin na ƙokarin tserewa zuwa ƙauyen ne aka sake harbo su da makami mai linzami na biyu,” in ji Rediyon Andalus.

    Al-Shabab ta ƙara da cewa mutane 12 kuma sun jikkata a harin da aka kai ta sama.

    Kawo yanzu dai babu wani tabbaci kan wannan ƙazamin harin da ake zargin an kai.

    • Abubuwan da ba ku sani ba game da ƙasar Somaliya
    • Yadda ƴan Somaliya ke amfani da manhajar koyon karatu
  2. Lazio ta nada Tudor sabon kociyanta ya maye gurbin Sarri

  3. Amurka ta ba da rahoton mutuwar babban jagoran Hamas

    ...

    Asalin hoton, MEDIA SOURCES

    Shugaban Hamas Marwan Issa ya mutu a wani hari da Isra'ila ta kai ta sama, in ji jami'in fadar White House Jake Sullivan.

    A matsayinsa na mataimakin kwamandan soji, Issa ya kasance shugaban Hamas mafi girma da ya mutu tun lokacin da aka fara yakin a ranar 7 ga Oktoba.

    Ƙungiyar Falasɗinawa da ke iko da Gaza ba ta ce komai ba a hukumance kan rahotannin mutuwarsa ba.

    Majiyoyin yaɗa labarai na Isra'ila sun rawaito cewa an kashe Mista Issa ne a wani hari da aka kai a wani katafaren rami da ke ƙarƙashin sansanin ƴangudun hijira na Nuseirat da ke tsakiyar Gaza a makon da ya gabata.

    Mataimakin kwamandan reshen soja na Hamas - Izzedine al-Qassam Brigades, an ɗauke shi a matsayin ɗaya daga cikin mutanen da Isra'ila ke nema ruwa a jallo.

    Ƙungiyar Tarayyar Turai wadda ta sanya shugaban Hamas cikin jerin sunayen ƴanta'adda, ta alaƙanta Issa kai tsaye da harin da ƙungiyar ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan 1,200.

    Isra'ila ta ɗaure shi na tsawon shekaru biyar a lokacin tada ƙayar baya na farko na Falasdinawa, sannan Hukumar Falasɗinawa ta tsare shi a shekarar 1997 har zuwa farkon intifada na biyu a shekara ta 2000.

    Sojojin Isra'ila sun kashe wasu manyan shugabannin Hamas tun ranar 7 ga watan Oktoba.

    Jagoran siyasar Hamas Saleh al-Arouri ya mutu sakamakon fashewar wani abu a yankin Dahiyeh da ke kudancin birnin Beirut. Ana daukar Isra'ila da alhakin kai harin.

    Mista Sullivan, mai ba da shawara kan harkokin tsaro na fadar White House, ya ce wasu shugabannin Hamas ana kyautata zaton suna ɓoye, "mai yiwuwa a cikin ƙarƙashin hanyar ƙasa ta Hamas" a Gaza.

    Ya yi alkawarin cewa Amurka za ta taimaka wa Isra'ila a ci gaba da farautar manyan shugabannin Hamas.

    • Isra'ila ta hana shigar da abinci Gaza - MDD
    • Ina ne Ƙudus kuma me ya sa ake taƙaddama kan shi?
  4. Yadda zafi ya tsananta a sassan ƙasashen Afirka

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Sudan ta Kudu da Kenya da Senegal da Mali sun fitar da sanarwar gargaɗi kan matsanancin zafi yayin da yanayin zafin da aka alaƙanta da ɗumamar yanayi ya bazu a yankunan Afirka.

    Sudan ta Kudu ta rufe makarantu domin kare yara yayin da ake sa ran yanayin zai kasi maki 45 a ma\aunin salshiyos.

    A Kenya, hukumar kula da yanayi a ƙasar ta gargaɗi yankunan da ke arewaci kan cewa za su fuskanci matsalar zafi da ta zarce digiri 30 kan ma'aunin salshiyos daga yau zuwa kwanaki 10 masu zuwa.

    An samu irin wannan yanayi na zafi a Senegal inda aka yi fama da matsanancin zafin na tsawon kwanaki a faɗin ƙasar kamar yadda kafar yaɗa labarai ta Dakaractu ta ruwaito.

    Hukumar kula da yanayi ta Senegal ta ce yanayin zai kai tsakanin digiri 44 da 45 a kan ma'aunin salshiyos musamman a yankin kudu maso gabashin ƙasar. Yayin da yankin tsakiya da kudu maso yamma za su kasance cikin yanayin zafin da ya haura maki 42 a ma'aunin salshiyos.

    A Mali ma, tsakiyar Bankass Circle da ke yankin Mopti ta sake nazarin jadawalin karatun makarantu a yanayin zafin, in ji kafar yaɗa labarai mai zaman kanta, Studio Tamani.

    Matsanancin zafin a gabashin Afirka dai an alaƙanta shi da yanayin El Nino da ke yawan faruwa idan koguna suka yi zafi kuma suka gangaro kan ƙasa a gaɓar ruwan Amurka ta kudu kuma ya afka cikin koguna.

    • Dalilin da ya sa zafi ya tsananta a wannan bazarar
    • An yi rana mafi tsananin zafi a tsawon shekara 60 a China
  5. Matan da suka maƙale a Oman cikin ƙangin bauta

  6. Za a sake tattaunawar neman tsagaita wuta a Gaza

    Nan gaba kaɗan ne masu shiga tsakani na Isra'ila za su fara tattaunawa a Qatar, da ake fatan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da Hamas a Gaza.

    Ɓangarorin biyu dai na fuskantar matsin lambar su dakatar da faɗa, da ba ta damar ƙarin agajin gaggawa a sassa daban-daban na Gaza.

    A ɓangare guda kuma shugaba Biden ya tattauna da Netanyahu kan gargaɗin kai hari Rafa ka iya zama babban kuskure.

    Wakilin BBC ya ce lokacin da shugaba Biden ya yi magana da Netanyahu, ya bayyana masa dalilin da ya sa ya yi matuƙar damuwa kan aikin sojin Isra'ila a birnin Rafah.

  7. Sojoji sun kuɓutar da mutum 16 da ƴanbindiga suka sace a Kajuru

    ..

    Asalin hoton, HQ Nigerian Army/Facebook

    Sojojin Najeriya ƙarƙashin runduna ta ɗaya sun kuɓutar da mutum 16 da ƴanbindiga suka sace a yankin Kajuru da ke jihar Kaduna.

    Sun kuma daƙile yunƙurin wata ƙungiyar miyagu na yin garkuwa da mutane.

    Cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na rundunar sojin, Manjo Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, rundunar ta ce sojojin da aka tura ƙarƙashin runduna ta ɗaya sun daƙile yunƙurin sace mutane tare da ceto mutanen da aka sace a yankin Tantatu da ke ƙaramar hukumar Kajuru a jihar Kaduna.

    A cewar sanarwar, sojojin sun kai samamen ne bayan bayanan sirrin da suka samu ranar Lahadi da daddare lokacin da suka bi sawun ƴanbindigar da suka sace wasu mutane a ƙauyen.

    "Da isar su wajen da lamarin ya faru, sojoji sun bi ƴanbindigar, inda suka yi musayar wuta daga bisani kuma suka kuɓutar da mutum 16 da aka sace," in ji sanarwar.

    "Sojojin na ci gaba da gudanar da bincike a cikin dazuka domin ganowa tare da tseratar da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su tare da murƙushe miyagun ayyukan ƴanbindigar."

    Shugaban hafsan sojojin ƙasa Taoreed Lagbaja ya yaba wa sojojin kan ƙoƙarin nasu tare da neman su ƙara ƙaimi wajen fatattakar masu aikata ta'addanci.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    • Rundunar sojin Najeriya ta kammala bincike kan harin Tudun Biri
    • Ƴan bindiga na tursasa wa manoma biyan haraji kafin girbi a arewacin Najeriya
  8. Maraba!

    Masu bin mu a wannan shafi muna muku maraba da shigowa shafin kai-tsaye na BBC Hausa.

    Nabeela Mukhtar Uba ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci, domin kawo muku halin da duniya ke ciki. Zan kasance tare da abokan aiki - Usman Minjibir da A'isha Babangida.

    Sai ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.