Shugaban MDD ya nemi a yi bincike kan mummunan kisan farar hular Gaza

Asalin hoton, AFP
Shugaban Majalisar Ɗinkin Duniya ya nemi a gudanar da bincike mai zaman kansa kan kisan mutum fiye da Falasɗinawa 100 lokacin raba kayan agaji a Gaza.
Aƙalla mutum 117 aka kashe kuma fiye da mutum 760 suka jikkata ranar Alhamis yayin da mutane suka kewaye motocin da ke ɗauke da kayayyakin.
Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya yi tur da lamarin inda ya ce farar hular na buƙatar agajin gaggawa.
Hamas ta zargi Isra'ila da buɗe wuta kan farar hula sai dai Isra'ila ta ce galibi sun mutu a turmutsitsi bayan da ta yi harbin gargaɗi.
A ranar Alhamis ne aka kasashen duniya suka soki Isra'ila inda shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce sojojin Isra'ila na kai wa farar hula hari.
Babban jami'i a kungiyar tarayyar Turai, Josep Borrel ya bayyana lamarin a matsayin kisan da ba za a amince da shi ba.
Da yake mayar da martani, Mr Guterres a shafinsa na intanet ya yi "tur da abin da ya faru ranar Alhamis a Gaza inda fiye da mutum 100 aka ba da rahoton sun mutu ko jikkata yayin da suke neman agaji."
- Ƙasashen duniya sun kaɗu da kisan Falasɗinawa fiye da 100
- An kusa ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza - Biden







