Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Burtaniya ta kashe sama da fan miliyan 300 kan harkokin tsaro a Afrika a 2023

    f

    Asalin hoton, Techeconomy

    Gwamnatin Burtaniya ta ce ta zuba kudi da suka kai fan miliyan 300 a wasu shirye-shiryen magance matsalar tsaro da wanzar da zaman lafiya, domin amfanin mutanen nahiyar da itra kanta Burtaniya.

    Minsitan kula da harkokin gwamnati Baroness Lucy Neville-Rolfe wadda ta zo Najeriya domin aikin haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu ce ta bayyana hakan cikin sanarwar da Atinku Akande-Alegbe jami’ar da ke ofishin yada labarai ta FCDO ta fitar.

    Ziyarar ta zo ne ‘yan kwanaki bayan da wani shirin haɗin gwiwar harkokin tsaro tsakanin ƙasashen biyu ya cimma yarjejeniya kan tsaron intanet, haɗin kan harkokin tsaro da yakin da ta’addanci da yancin ɗan adam da haɗin kai tsakanin jami’an tsaro da fararen hula.

    A Arewa maso Gabashin Najeriya kudin da Burtaniya ta zuba sun taimaka wa sama da mutum 500 da suka gujewa rikicin aka ba su wuraren zama.

    Tataimaka wajen koyar da sana’o’in hannu da harkokin addinai da wayer da kan al’umma kan harkokin shaye-shaye.

  2. Jami'an Isra'ila sun kashe Falasdinawa biyu Gabar Yammacin Kogin Jordan

    g

    Asalin hoton, Getty Images

    Jami'an Lafiya a Falasdin sun ce dakarun Isra'ila sun kashe mutane biyu a Gabar Yamma da Kogin Jordan.

    Mutanen sun rasa rayukansu yayin samamen da sojin Isra'ila suka kadamar a sansanin 'yan gudun hijira na Tulkarm da ke Arewacin Gabar Yamma.

    Sojojin Isra'ila sun bayana cewar dakarunsu da suka je sansanin don kamo wasu da ake zargi, sun mayar da martani ne bayan an jefa musu wani abin fashewa.

    Ma'aikatar Lafiya ta Falasdin ta ce kusan mutane dari hudu Sojin Isra'ila da Yahudawa 'yan kama guri zauna suka kashe a a Gabar Yamma da Kogin Jordan tun farkon yakin a Gaza.

  3. Mun ƙara tsaro a birnin Goma na Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo - MDD

    A

    Asalin hoton, Reuters

    Dakarun Wanzar da Zaman Lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a Gabashin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kwango, sun ce sun ƙara tsaro a kewayen Goma babban birnin yankin, wanda ke fama da harre-haren 'yan tawaye.

    Kakakin kungiyar rundunar tsaron ta MONUSCO Kadagni Mensah ya ce kungiyar M23 wadda Rwanda ke goyon baya ta kaddamar da hare-hare da dama a cikin kwanaki goma da suka gabata a garin Sake da ke kusa da yankin da hanyoyin Gabas maso Yammaci da Arewa maso Kudu suka hadu.

    Washington ta dora alhakin abinda ya ke faruwa kan Rwanda, ta bukaci Kigali ta janye dakarunta, to amma mazauna 'kauyuka sun ce gungun yan tawaye na zuwa.

    Dubban mutane ne suka rasa matsugunansu. A ranar Asabar ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta buƙaci M23 ta dakatar da hare-hare cikin gaggawa, sannan ta yi Allah wadai da goyon bayan da Rwanda ta ke ba yan tawayen.

  4. Isra'ila za ta janye jakadanta daga Brazil kan sukar da shugaba Luis ya yi mata

    ,

    Asalin hoton, Netanyahu

    Ma'aikatar harkokin wajen Isra'ila ta ce za ta yi wa jakadanta na Brazil kiranye gobe sakamakon kalaman shugaban ƙasar kan yaƙin Gaza.

    Shugaba Inacio Lula da Silva ya yi kakkausar suka ga yadda Isra'ila ke yaƙi a Gaza, inda ya kwatanta amin da take yi da irin wanda Hitker ya yi na "yunkurin ƙarar da Yahudawa".

    Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya mayar da martani kan kalaman yana cewa " wannan nuna ƙabilanci ne kwatanta kisan da aka yi wa Yahudawa da kuma ƙoƙarin Isra'ila na kare kanta. Kwatanta tsakanin Isra'ila da Nazi da kuma Hitler a wajenmu wuce iyaka ne."

    Ministan harkokin wajen Isra'ila ya wallafa a shafinsa na X cewa : "babu wanda zai sa Isra'ila ta yi watsi da 'yancinta na kare kanta."

  5. Biden ya yi wa Zelensky alƙawarin taimakon dala biliyan 60

    g

    Shugaban Amurka Joe Biden ya tabbatar wa Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky zai ba shi taimakon soji da ya kai na dala biliyan 60.

    Sai majalisar dokokin Amurka ta amince za a bayar da taimakon, amma Biden ya shaida wa Zelensky cewa yana da kwarin gwiwar za a amince da taimakon.

    Amurka ta zargi janyewar da sojin Ukiraine suka yi daga Avdiivka da ƙarancin goyon bayan majalisar dokoki.

    A ranar Asabar Ukraine ta fice daga birnin, wanda yaje kusa da Donetsk inda Rasha ta mamaye.

  6. Shugaban Brazil ya kwatanta abin da Isra'ila ke yi a Gaza da irin na "Hitler kan Yahudawa"

    g

    Shugaban ƙasar Brazil Luis Inacioula da Silva ya zargi Isra'ila da aikata "kisan kare dangi" a Gaza, inda ya kwatanta abin da suke yi a Gaza da "irin abin da Adolf Hitler ya yi wa Yahudawa."

    Shugaba Luis ya bayyana hakan ne a Addis Ababa, inda ya halarci taron kungiyar Tarayyar Afrika, yana cewa abin da yake faruwa a Gaza ba yaƙi ba ne tsakanin soja da soja, yaƙi ne tsakanin sojojin da suka samu horo da kuma mata da yara ƙanana.

    Ya ce babu wani mai kama da yakin Gaza tuntuni "Kamar yadda Hitler ya so ya kawar da Yahudawa baki daya daga doron duniya".

  7. WHO ta ce asibitin Nasser na Gaza ya daina aiki bayan harin Isra'ila

    .

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta ce asibitin Nasser da ke Gaza ya daina aiki bayan wani hari da Isra'ila ta kai masa.

    A ranar Alhamis ne rundunar sojin Isra'ila ta shiga ginin asibitin, bayan da ta ce ta samu bayanan sirri cewa ana tsare da Isra'ilawan da Hamas ke garkuwa da su a cikin asibitin.

    WHO ta ce ba a ba ta damar shiga cikin asibitin don tantance yanayin da asibitin ke ciki.

    Isra'ila na ta mayar da hankali wajen kai hare-hare kan ƙungiyar Hamas a kudancin Gaza a Khan Younis, sannan ta nuna alamun ci gaba da kai hare-hare zuwa kudancin Rafah.

  8. Ko kun san muhimmancin yawan yin jima'i ga lafiyar ɗan adam?

  9. Kamfanin X ya amince zai biya tsoffin ma'aikatansa na Ghana

    .

    Asalin hoton, X

    Kamfanin X, da a baya aka fi sani da Twitter ya amince zai biya tsoffin ma'aikatansa da suka yi aiki a ofishinsa da ke Ghana, bayan lokaci mai tsawo da aka ɗauka ana shari'a kan batun.

    Ma'aitan kamfanin da dama ne aka sallama daga bakin aiki bayan da attajirin ɗan kasuwar nan Elon Musk ya sayi kamfanin a shekarar 2022.

    Sai dai kamfanin bai bayyana adadin kuɗin da kowane ma'aikacin zai samu ba, da kuma lokacin da zai biya kuɗin.

    To amma lauyoyin ma'aikatan sun ce sun cimma yarjejeniyar biyan ma'aikatan kuɗaɗe sallamarsu, tare da kuɗin guzuri ga ma'aikatan da ba 'yan Ghana ba, don su samu abin da za su koma ƙasashensu.

    A cikin sanarwar da lauyoyin suka fitar, sun ce dokokin Ghana sun yi tanadin cewar dole a tabbatar ma'aikatan da aka sallama daga aiki, ba su faɗa cikin matsin rayuwa ba.

    Kamfan sada zumuntar ya gaza yin aiki da umarnin da ofishin shugaban ƙwadagon Ghana ya ba shi, na bai wa ma'aikatan kuɗin sallamar, kamar yadda dokokin ƙwadagon ƙasar suka tanada.

    Lauyoyin sun ce tsoffin ma'aikatan na cikin murna da farin ciki da sabuwar yarjejeniyar da aka cimma da kamfanin.

    Ma'aikata da dama ne dai suka kaɗu da matakin kamfanin na X ya ɗauka na rufe ofishinsa guda ɗaya tilo a Afirka tare da sallamar ma'aikatansa a 2022.

  10. Zaɓen Iran: Jagoran addinin Iran ya shawarci 'yan takara su kauce wa ɓatanci

    .

    Asalin hoton, IRN

    Jaroran addini na ƙasar Irana Ayatollah Ali Khamenei, ya shawarci 'yan takarar da za su fafata a zaɓen ƙasar da ke tafe da su guji yi wa juna ɓatanci.

    Mista Khamenei ya yi kiran ne a lokacin wani taro da ya gudanar da wata ƙungiyar mutanen gabashin Azerbaijan kan zaɓukan da ke tafe.

    Ya ce "Ya kamata mutanen da suka shiga zaɓukan su kauce wa kalaman ɓatanci da zagi da cin mutuncin juna.''

    Jagoran addinin ya bayyana zaɓukan a matsayin ''hanyar kawo sauyi''.

    "A koyaushe ana samun nasarar gudanar da zaɓuka cikin doka da kwanciyar hankali a ƙasarmu, don haka a wannan karon ma muke fatan samun hakan'', in ji shi.

    A ranar 11 ga watan Maris ne za a gudanar da zaɓuƙan majalisar dokokin ƙasar ta 12.

    Tuni da majalisar shura ta ƙasar ta soke takarar manan 'yan siyasar ƙasar a wannan karo.

    Hassan Rouhani da Mostafa Pourmohammadi na daga cikin manyan 'yan siyasar ƙasar da aka soke takararsu.

    Masu lura da al'amura sun yi hasashen samun ƙarancin fitowar masu zaɓe a lokacin zaɓukan, saboda rashin gamsuwa da wasu al'amuran ƙasar, da abin da ya faru bayan kisan Mehsa Amini a lokacin da take tsare a hannun jami'an 'yansandan ƙasar.

  11. Wace ƙasa ce ta fi ƙanƙanta a duniya, da tarihin yaren Margi

    Shirin Amsohin takardunku na wannan makon - wanda Aisha Shariff Bappa ta gabatar - ya binciko ƙasar da ta fi kowace ƙasa ƙanƙanta a duniya.

    Sannan shirin ya kuma taɓo matsalar ɓacin rai, dalilansa da kuma illolinsa da dabarun kauce masa.

    Daga ƙarshe kuma shirin ya duba tarihin yaren Margi, asalinsa da kashe-kashen yaren da kuma irin al'adun masu amfani da harshen.

    Bayanan sautiLatsa hoton da ke sama domin sauraron shirin
  12. Trump ya fara sayar da takalmi bayan cin sa tarar dala miliyan 355

    .

    Asalin hoton, Reuters

    Tsohon shugaban Amuka Donald Trump ya ƙaddamar da sabon kamfanin sayar da takalma a birnin Philadelphia na jihar Pennsylvania.

    Yayin da yake magana cike ga ƙwarin murya, mista Trump ya sha sowar murna daga waɗanda suka halarci bikin ƙaddamar da sabon kamfanin a lokacin da ya gabatar da wasu samfurin takalman masu launin ruwan gol da kuɗinsu ya kai dala 399.

    Ƙaddamar da sabon kamfanin takalman na zuwa ne kwana guda bayan wata kotu ta umarci ya biya tarar kusan dala miliyan 355 ga hukumomin jihar New York saboda samunsa da yin ƙarya kan darajar kadarorinsa.

    Trump ne aka fi sa wa ran zama ɗan takarar jam'iyyar Republican a zaɓen shugaban ƙasar na watan Nuwamba mai zuwa.

    .

    Asalin hoton, Reuters

  13. Hauhawar farashi a Najeriya na neman wuce tunanin mutane - Masana

    .

    A Najeriya, masana na ganin cewa matukar ba ƙwararan matakan da suka kamata aka bi ba, to da wuya a magance matsalar ta hauhawar farashin kaya da ta tsadar rayuwa a kasar.

    Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da 'yan ƙasar ke ci gaba da kokawa game da hauhawar farashin kayayyaki da tsadar rayuwa.

    Hukumomi dai na ta bayar da tabbacin cewa suna bin matakan da suka dace domin shawo kan lamarin.

    Farfesa Kabiru Isa Dandago, wani masani a fannin ƙididdigar kuɗi da tattalin arziki a jami'ar Bayero ta Kano, yana ganin cewa da wuya a iya daƙile hauhawar farashin kayyaki a Najeriya cikin ƙaramin lokaci.

    Masanin ya yi gargaɗin cewa matuƙar ba a hankali ba wannan lamari ba zai zama alkairi ba.

    Ga dai karin bayanin da ya yi wa BBC

    Bayanan sautiLatsa hoton da ke sama domin sauraron hirar
  14. 'Yan bindiga sun kai hare-hare tare da sace fiye da 30 a Kaduna

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotonni daga Najeriya na cewa 'yan bindiga sun auka wa garuruwan Gwada da Kwassam a ƙananan hukumomin Igabi da Kauru da ke jihar Kaduna, inda suka kashe mutum tara da raunata a ƙalla bakwai, tare kuma da yi garkuwa da fiye da mutum 30, ciki har da tsohon daraktan babban bankin ƙasar CBN.

    Cikin wata sanarwa da kakakin Ƙungiyar Al'ummomin Yankin Kudancin Kaduna, (SOKAPU), Josiah Abraks, ya fitar ya tabbatar da harin 'yan bindigar a garin Kwassam .

    Ya ce maharan sun yi garkuwa da kimanin mutum 50 a wani hari da suka kai ƙauyen Sabon Layi.

    Abraks ya yi kira ga gwamnatin jihar da jami'an tsaro da su ɗauki mataki kan maharan da ke yawan kai wa yankunan kudancin Kaduna hare-hare.

    To sai dai cikin wata sanarwa daga gwamnatin jihar ta fitar ta hannun kwamishin lura da harkokin tsaron cikin gida, Samuel Aruwan, gwamnatin ta tabbatar da hare-haren sai da ba ta yi ƙarin haske kan waɗanda suka mutu ko aka sace ba.

    Sanarwar ta ambato gwamnan jihar, Uba Sani na Allah wadai da hare-haren tare da jajanta wa mutanen da lamarin ya shafa, yana mai kira ga sojoji da su tsananta hare-hare kan 'yanbindigar da ke addaban yankin.

    Gwamnan ya kuma aike da tawagar wakilan gwamnati ƙarƙashin jagorancin kwamishin lura da al'amuran tsaron cikin gida, garin da lamarin ya faru, inda suka gana da sarakunan gargajiyar yankin da jagororin addini na yankin.

    Jihar Kaduna dai na daga cikin jihohin ƙasar da ke fama da matsalar tsaro, inda 'yan bindiga ke sace mutane domin neman kuɗin fansa.

  15. Dan arewacin Najeriya da ya zama malamin harshen Indiya

    Duk da cewa Indiya ba bakon harshe ba ne a kasar Hausa amma ba kasafai ake samun wanda ya kware har yake koyar da shi ba a cikin al’umma.

    Salman Muhammad Waddare ya shaida wa BBC cewa matukar sha’awar harshen ne ya kai shi ga wannan matsayi.

    Bayanan bidiyo, Latsa hoto da ke sama domin kallon bidiyon
  16. Legas za ta hana amfani da soson tekawe daga gobe Litinin

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin jihar Legas ta ce daga gobe Litinin 19 ga watan Fabrairu za ta fara aiwatar da dokar haramta amfani da robar sayar da abinci ta takway a fain jihar.

    Kwamishin muhalli da albarkatun ruwa na jihar, Tokunbo Wahab, ne ya bayyana haka a lokacin ganawa da shugabannin kasuwannin jihar.

    Haka kuma cikin wata sanarwar da mai magana da yawun ma'aikatar, Kunle Adeshina, ya fitar ranar Asabar, ya ce kwamishinan muhallin ya ce jami'an hukumar tsaftar muhalli da jami'an 'yansanda da sauran hukumomin da lamarin ya saf za su zagaya kasuwanni domin kama robobin da ake sayarwa a shaguna.

    Sanarwar ta yi kira ga 'yan kasuwa da su guji sayar da abinci a kan layukan dogo da titunan mota.

    ''Dole ne mu tsftace kasuwanninmu daga abin da zai guata mana ita'', in ji kwamishinan.

    Ya ƙara da cewa dole a raba shara daga kasuwannin jihar, do inganta lafiyar al'umma.

  17. Tsohon firaministan Thailand ya fara zaman ɗaurin talala

    ..

    Asalin hoton, AFP VIA GETTY IMAGES

    Tsohon firaministan Thailand, Taksin Shinawatra, ya isa gidansa da ke Bangkok bayan an sake shi daga zaman gidan yari zuwa ɗaurin talala.

    An sallamo hamshaƙin attajjirin ne daga asibiti, inda yake zama tun bayan da aka yanke masa hukuncin ɗaurin shekara guda kan laifin cin hanci da rashawa da rashin mutunta ofishinsa.

    Mista Taksin ya koma Thailand bayan kwashe fiye da shekara 15 yana zaman gudun hijira bayan da sojoji suka hamɓarar da gwamnatinsa a shekarar 2008.

    Ya kwashe tsawon lokacin ne yana zaune tsakanin Birtaniya da Haɗaɗdiyar Daular Larabawa.

    Jam'iyyar danginsa ta 'Pheu Thai Party' ce ke mulkin ƙasar a halin yanzu.

    Tsohon firaministan ya kasance mutumin da aka samu rarrabuwar kai a kansa a ƙasar, inda manyan masu kuɗi 'yan siyasa ke ƙinsa, yayin da miliyoyin talakawan ƙasar, musamman mazauna ƙauyuka ke matuƙar sonsa saboda fitattun manufofinsa.

    Mista Thaksin ya kasance firaministan Thailand na farko da ya jagorancin ƙasar wajen gudanar da babban zaɓen ƙasar, da ya samar da zaɓaɓɓiyar gwamnati.

  18. Biden ya buƙaci majalisa ta amince da tallafin soji ga Ukraine

    .

    Asalin hoton, .

    Shugaban Amurka Joe Biden ya yi kira ga majalisar dokokin ƙasar ta amince da gagarumin tallafin soji ga Ukraine.

    Kiran na zuwa ne bayan da dakarun Rasha suka mamaye garin Avdivka da ke yankin Ukrane.

    Fadar White House ta ɗora alhakin hakan kan ƴan siyasar Amurka sakamakon gazawa wajen samar wa Ukraine isassun makamai.

    Shugaban Amurkan dai na son ba Ukraine tallafin dala biliyan sittin, tallafin da ya ce ana tsananin buƙata.

  19. Tattaunawar tsagaita wuta kan rikicin Gaza na jan ƙafa - Qatar

    .

    Asalin hoton, Reuters

    Qatar ta bayyana tattaunawar cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas da cewa tana jan ƙafa.

    Manyan jami'an ƙasashen duniya ne ke tattaunawa a birnin Alƙahira domin cimma yarjejeniyar.

    Firaministan Qatar Mohammad bin Abdulrahman Al Thani ya ce har yanzu yana da ƙwarin guiwar cewa za a iya cimma yarjejeniyar, sai dai lokaci na ƙurewa.

    Sai dai Firaministan Isra'ila Benyamin Netanyahu na ci gaba da jaddada aniyarsa ta ci gaba da yaƙi a Gaza.

  20. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa barkanmu da hutun rƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kun wayi gari lafiya, tare da farin cikin sake kasancewa da ku a wannan lokacin don kawo muku irin wainar da ake toyawa a faɗi duniya.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.