Wata
babbar kotu da ke zaman ta a birnin Kano ta buƙaci a yi wa Hafsat Surajo
(Chuchu) gwajin taɓin hankali a ci gaba da shari’ar da ake yi mata kan zargin kisan wani matashi mai suna Nafi'u
Hafiz.
Kotu ta ɗauki wannan
mataki ne bayan da Hafsat ta ƙi cewa uffan a lokacin da aka karanta mata
tuhumar da ake yi mata.
Kotun ƙarƙashin jagorancin
mai shari’a Zuwaira Yusuf ta buƙaci a samu likitan ƙwaƙwalwa da zai duba
lafiyar Hafsat a inda ake tsare da ita.
Tun farko an karanta wa
Hafsat laifukan da ake tuhumar ta da su, sai dai ba ta ce komai ba a lokacin da
kotu ta tambaye ta ko ta fahimci abin da ake nufi ko a’a, balle ma ta amsa ko
tana da hannu a cikin abin da ake zargin nata da shi ko a'a.
Yanzu haka kotun za ta
jira sakamakon gwajin da likita zai yi wa Hafsat kafin ci gaba da sauraron
shari’ar.
A cewar kotu, dole ne a
tantance lafiyar duk wanda ake tuhuma kafin ci gaba da shari’a, kasancewar "ba a yin shari'a da mai taɓin hankali."
Wannan ne karo na farko
da ake karanto wa Hafsat tuhume-tuhumen da ake yi mata a gaban babbar kotun.
An gabatar da ita ne a
kotun tare da mijinta da kuma wasu mutum biyu da ake zargi da hannu wajen
aikata laifin.
Haka nan a lokacin
zaman na yau Alhamis, lauyoyin waɗanda ake tuhuma sun gabatar wa kotu buƙatar
bayar da belin mjin na Hafsat da sauran mutum biyun, sai dai kotun ta ce za ta
sanya ranar sauraron buƙatar tasu.
A watan Disamban shekarar da ta gabata ne rundunar ƴansanda a jihar Kano ta bayyana cewa jami’anta sun kama
Hafsat Surajo ƴar shekara 24 da ke Unguwa Uku bisa zargin kashe Nafi'u Hafiz,
ɗan shekara 38 a gidanta na aure.
Haka zalika binciken ƴansandan ya kai ga kama mijin
matashiyar, Dayyabu Abdullahi mai shekara 38, sai kuma Mallam Adamu mai shekara
65 da kuma ƙarin wani mutum ɗaya.
Tun a wancan lokaci ne kotu ta bayar da
umarnin ajiye Hafsat a gidan kaso.
Bayan kammala zaman kotun na yau an
mayar da Hafsat da sauran waɗanda ake tuhuma zuwa gidan gyaran hali domin ci
gaba da tsare su.