Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Nabeela Mukhtar Uba and Haruna Kakangi

  1. Kotun ƙoli ta tabbatar da nasarar Fintiri a matsayin gwamnan Adamawa

    Kotun ƙoli ta tabbatar da zaɓen gwamna Ahmadu Fintiri a matsayin halastaccen gwamnan jihar Adamawa.

    Mai shari’a John Okoro wanda ya karanta hukuncin a ranar Laraba ya yi watsi da ƙarar da ƴar takarar gwamna a jam’iyyar APC, Aisha Dahiru wadda aka fi sani da Binani ta shigar kan rashin cancanta.

    A yayin da kotun ta yi watsi da ƙarar, kwamitin alƙalai biyar karkashin jagorancin Mai Shari’a John Okoro ta bayyana cewa, abin da Kwamishinan Zabe (REC), Hudu Ari ya aikata, ta hanyar faɗin sakamakon zaɓe kafin kammala ƙirga ƙuri'a - wani abu ne na rashin gaskiya da kuma aikata laifi.

    Okoro ya ci gaba da cewa, babban jami’in zaɓe na jihar ne ya kamata ya bayyana sakamakon zabe, domin a kauce wa hargitsi da rudani.

    • Gwamna Fintiri ya ce ya ji takaicin abin da jami'in INEC ya yi a Adamawa
    • Adamawa: Zaɓen da aka kammala ƙura ba ta kwanta ba
  2. An aiwatar da hukuncin kisa kan ma'auratan da suka halaka ƴaƴansu don su ji daɗin soyayya

    Ƙasar China ta zartar da hukuncin kisa kan wani mutum da matarsa bisa laifin kashe ƙananan ƴaƴansu biyu domin su ji daɗin soyayya da more rayuwa.

    Lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a faɗin kasar ta China.

    Mutumin dai ya jefa diyarsa ƴar shekara biyu da ɗansa mai shekara ɗaya ta tagar wani gida, inda suka yi kokarin bayyana mutuwarsu a matsayin tsautsayi.

    Hukuncin kisan ma'auratan ya ɗauki hankalin jama'a sosai a shafukan sada zumunta na kasar, inda da yawa ke ganin hukuncin ya yi daidai da laifin da suka aikata.

    • An kashe yara a harin da matashiya ta kai kan wata makaranta a Amurka
    • Yadda za ku kare yaranku daga cutuka bayan komawa hutun makaranta
  3. Sojoji sun kuɓutar da mutum uku da aka yi garkuwa da su a jihar Taraba

    Sojojin Bataliya ta 114 ta Sojojin Najeriya sun ceto wasu mutane uku da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Jalingo, babban birnin jihar Taraba.

    Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta 6 Brigade, Leiutenant Olubodunde Oni ya fitar ga manema labarai.

    Sanarwar ta ce sojojin sun yi aiki ne da bayanan sirri game da zirga-zirgar ƴan bindigar tare da waɗanda suka sace daga Ardo-Kola zuwa Yoro, sannan suka tura dakaru a kauyen Apawa da ke karamar hukumar Yoro zuwa yankin tare da fatattakar 'yan bindigar.

    Ya kara da cewa sojojin sun fafata da ƴan bindigan, inda hakan ya tilasta musu yin watsi da mutanen uku da suka sace.

    Oni ya ce "Mun yi farin cikin bayar da rahoton cewa mutanen da aka ceto sun hadu da iyalansu yayin da muke ci gaba da bin sawun masu garkuwa da mutanen."

  4. Ƙungiyar da ke ƙawance da Iran ta dakatar da kai hari a Amurka

    Wata kungiyar 'yan bindiga ta Iraƙi da ake zargi da kai hari da jiragen yaki mara matuki a kasar Jordan da ya kashe sojojin Amurka uku ta ce ta dakatar da kai farmaki kan Amurka.

    Ƙungiyar Kataib Hezbollah da ke da alaƙa da Iran da ta dauki alhakin kai harin a ranar Lahadin da ta gabata, ta ce ta yi hakan ne don hana gwamnatin Iraki shiga kunya.

    Shugaban Amurka Joe Biden ya ce ya yanke shawarar yadda zai mayar da martani kan harin amma bai yi ƙarin haske ba.

    Iran ta yi gargaɗin cewa za ta mayar da martani kan duk wani hari da aka kai mata kan "muradinta".

    Da yake ba da shawarar cewa ba za ta sake kai wani hari kan Amurka ba, babban sakataren kungiyar Hizbullah Kataib Abu Hussein al-Hamidawi ya bayyana a cikin wata sanarwa a ranar Talata cewa: "A yayin da muke sanar da dakatar da ayyukan soji da na tsaro a kan dakarun Amurka - domin hana abin kunya na gwamnatin Iraki - za mu ci gaba da kare mutanenmu a Gaza ta wasu hanyoyi."

    Kafar yaɗa labarai ta CBS, abokiyar huldar Amurka ta BBC ta bayyana cewa an kashe sojojin Amurkan uku ne a kan iyakar Jordan da Syria da wani jirgi mara matuki da aka ce an yi shi a Iran.

    • Abin da ya sa Amurka ta kai hare-hare kan ƴan a waren da Iran ke goyon baya a Iraki
    • Burtaniya da Amurka sun ce Iran za ta yaba wa aya zaki kan harin jirgin ruwan Isra'ila
  5. Majalisar dattawa ta yi sammacin manyan hafsoshin sojin Najeriya kan matsalar tsaro

    Majalisar dattawa ta yi sammacin manyan hafsoshin tsaron Najeriya game da kalubalen tsaro da ke ci gaba da ta'azzara a fadin kasar.

    Yan majalisar sun yi wannan kira a karkashin murya guda bayan wani zaman gaggawa da suka yi bayan dawowarsu bakin aiki karon farko a wannan shekarar.

    Majalisar dattawan ta yi zaman gaggawar ne bayan da shugaban masu rinjaye na majalisar Sanata Opeyemi Bamidele ya gabatar da kuduri a madadin sanatocin kan yanayin tsaro a Najeriya.

    Bayan shafe kusan sa'a biyu suna taron sirri, majalisar ta sake haduwa tare da yanke shawarar gayyato manyan hafsoshin tsaro a mako mai zuwa game da karuwar rashin tsaro a kasar.

    Manyan hafsoshin tsaron sun hada da babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa da shugaban rundunar sojin kasa, Leftenant Taoreed Lagbaja da shugaban rundunar sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar da shugaban rundunar sojin ruwa Vice Admiral Emmanuel Ogalla.

    Majalisar ta kuma dage zamanta zuwa 6 ga watan gobe na Fabarairu domin bai wa yan majalisar damar yin zabe a zaben cike gurbi na ranar Asabar.

    A baya-bayan nan, an ga karuwar matsalar tsaro a Abuja, babban birnin kasar da jihar Filato da wasu sassan Najeriya da aka samu karuwar garkuwa da mutane don kudin fansa da kashe-kashe na baya-bayan nan shi ne kisan wasu sarakunan gargajiya da kuma sace daliban makaranta da malamai a jihar Ekiti.

    Ko a jiya, tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya soki Shugaba Bola Tinubu da yin tafiye-tafiye yayin da kasar ke fama da matsalolin tsaro sai dai a martaninta, gwamnati ta ce tana yin duk mai yiwuwa domin dakile matsalar.

    • Rikicin Filato: 'Na ga gawawwaki yashe a kan titi'
    • Yadda ƴan bindiga suka yi awon-gaba da ango da amaryarsa a Zamfara
    • Yadda sojin Najeriya suka yi wa ƴanbindiga ruwan wuta a Kaduna
  6. Maraba!

    Ma'abota wannan shafi na Kai Tsaye da BBC Hausa ke kawo muku a kullum, barkan mu da warhaka. Da fatan mun wayi gari lafiya a wannan rana ta Laraba - tabawa ranar samu.

    A yau ma, shafin zai wallafa muku rahotanni da labarai na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.

    Sai ku kasance tare da mu tun daga yanzu har zuwa lokacin da za mu rufe shafin na Kai Tsaye.

    Akwai shafukanmu na sada zumunta da za ku iya zuwa domin karanta karin labarai da kuma kallon bidiyo.