Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku bubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Haruna Kakangi and A'isha Babangida

  1. Angola ta musanta alaƙa da jirgin ruwan da mayaƙan Houthi suka kai wa hari

    ...

    Asalin hoton, Indian Navy

    Kamfanin mai na Angola Sonangol ya yi watsi da rahotannin da ke cewa wani jirgin ruwa da mayakan Houthi suka kai wa hari a makon jiya a mashigin tekun Aden na cikin jiragensa.

    Jirgin ruwan da ke da alaka da Birtaniya ya shafe sa'o'i da dama yana cin wuta a ranar Juma'ar da ta gabata a mashigin tekun Aden bayan da 'yan Houthi suka harba makami mai linzami.

    Ƙungiyar da Iran ke marawa baya, wadda ke da hedkwata a Yemen, ta ce ta kai hari kan Marlin Luanda ne a matsayin martani ga "harin haɗin gwiwar da Amurka da Birtaniya suka kai".

    Musantawar ta zo ne a matsayin martani ga rahotannin kafafen yada labarai na Angola da ke alakanta jirgin ruwan Marlin Luanda da Sonangol.

    Kamfanin Sonangol ya sanar da jama'a cewa jirgin ruwan Marlin Luanda, wanda makami mai linzami ya harbo kwanan nan a cikin tekun Bahar Maliya, ba ya cikin tashoshin jiragen ruwa mallakar kamfani ko hayarsa," in ji kamfanin a cikin wata sanarwa da kafafen yada labarai na cikin gida suka gani.

    Marlin Luanda, wanda ke aiki a madadin Trafigura mai siyar da kayayyaki ta Singapore, yana dauke da tutar tsibirin Marshall.

    Trafigura na ɗaya daga cikin manyan masu samar da dizal da dizal na jirgen ruwa zuwa Angola.

    Har ila yau, yana da hannun jari a kamfanin makamashi na Puma, wanda ke kula da gidajen mai na Pumangol a Angola.

    Sauran masu hannun jari a Puma Energy sun hada da Sonangol.

  2. Yar Najeriya ta soma bulaguro daga London zuwa Legas a mota

    ...

    Asalin hoton, Pelumi Nubi/Instagram

    Wata yar Najeriya Pelumi Nubi ta soma wata tafiya daga birnin Landan zuwa Legas ta mota - tafiyar da ke da nisan fiye da kilomita 7,000.

    Daga Ingila, Ms Nubi za ta tsallaka Faransa da Spaniya kafin shiga Africa ta kasar Maroko.

    "Bayan nan, za ta bi ta Sahara ta shiga Mauritania da Senegal da The Gambia da Guinea- Bissau da Guinea da Saliyo da Laberiya da Mali da Burkina Faso da Ivory Coast da Ghana da Togo da Benin sai kuma Najeriya zuwa Legas," in ji Ms Nubi.

    Ba wannan ne karon farko ba da ake irin wannan kudiri na tafiye-tafiye da mota daga Landan zuwa Legas, sai dai Ms Nubi ta ce tana tunanin ita ce bakar fata mace ta farko da ta yi yunkurin yin haka.

    "Sai dai ta ce wannan ba batun kafa tarihi bane. Batu ne na nuna wa duniya wani abu da ba a yi tunanin za a iya ba," kamar yadda ta ce a lokacin da ta sanar da kudurin nata a watan Nuwamban bara.

    A makon da ya gabata, Ms Nubi ta ce ta dauki tsawon shekara daya tana shiri da tara kudi da kuma tsara yadda bulaguron zai kasance.

    Ms Nubi wadda ke son tafiye-tafiye ta ziyarci kasa 80 kuma tana yawan nuna tafiye-tafiyen da ta yi a shafukanta na sada zumunta.

    • Me ya sa ƴan Najeriya ke rige-rigen shiga Kundin Bajinta na Guiness?
    • Gwanar girki 'yar Najeriya da ke burin kafa tarihi a duniya
  3. An yanke wa tsohon Firaiministan Pakistan shekara 10 a gidan yari

    ..

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Magoya bayan jam'iyyar PTI ta Imran Khan sun halarci wani gangami gabanin babban zabe a Karachi

    An yanke wa tsohon Firaiministan Pakistan Imran Khan hukuncin shekara 10 a gidan yari a karar da ake zarginsa da fitar da wasu bayanan sirri na kasa.

    Mr Khan wanda aka hambarar daga mukamin Firamiminista a 2022, yana zaman gidan yari na shekara uku bayan da aka same shi da hannu a rashawa.

    Ya bayyana tuhume-tuhumen da ake masa a matsayin kullin siyasa.

    Samun sa da laifi karkashin dokar bayanan sirri na zuwa ne mako daya kafin babban zaben da aka haramta masa tsayawa takara.

    Kotun ta musamman ta kuma yanke wa tsohon ministan harkokin waje Shah Mahmood Qureshi shekara 10 a gidan yari.

    Karar ta shafi zargin fitar da wasu bayanan sirri da jakadan Pakistan a Amurka ya tura zuwa Islamabad lokacin da Mr Khan yake Firaiminista.

    Ya yi zargin sakon na kunshe da wata barazana daga Amurka na kifar da gwamnatinsa, zargin da Amurkar ta musanta.

    Jam'iyyar PTI ta Mr Khan ta ce za ta kalubalanci hukuncin inda kuma ta kira karar a matsayin mara tushe.

    A ranar 8 ga watan Fabrairu ne za a yi babban zabe a Pakistan daidai lokacin da jam'iyyar PTI ke zargin hukumomi sun hana ta yakin neman zabe. Mr Khan ya kasance a gidan yari tun watan Agusta.

  4. An yanke wa mutum 12 daurin rai da rai saboda kisan wani soja a Ghana

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Wata kotu a Ghana ta yanke wa mutum 12 hukuncin daurin rai da rai bayan da ta same su da laifin kisan wani soja shekaru bakwai da suka gabata.

    Suna cikin mutum 14 da ake zargi da cinna wa sojan mai suna Manjo Maxwell Mahama wuta a Mayun 2017, a yankin Denkyira Obuasi, lamarin da ya tayar da kura a kasar.

    Babbar kotu a Accra, babban birnin kasar ta samu mutanen 12 da laifin kisa da hada baki wajen yin kisa da kuma taimakawa a yi kisan.

    Sun hada da wani dan siyasa wanda ake zargi da tattara jama'a somin kai wa sojan hari a lokacin da yake motsa jiki.

    Biyu cikin wadanda ake zargi kuma an wanke su bayan da kotu ta gano ba su da laifi.

    Sojan mai shekara 32 yana bakin aiki a yankin Denkyira Obuasi da ke tsakiyar kasar lokacin da mutanen suka far masa saboda zargin cewa dan fashi da makami ne.

    Yana daga sojojin da aka tura zuwa yankin domin kare wurin hakar ma'adinai.

    Kisan sojan dai ya fusata mutane a fadin kasar. Kuma bayan faruwa lamarin ne aka kama fiye da mutum 50 da ake zargi, sai dai bayan tantance su an tuhumi mutum 14 a cikinsu.

    • An tanadi hukuncin ɗaurin rai da rai ga duk mutumin da ya ce mai neman jinsi ne a Uganda
    • Yadda kotu ta yanke wa masu fyade hudu hukuncin daurin rai-da-rai a Jigawa
  5. Kamfanin Elon Musk ya dasa wa majinyaci na'urar taimaka wa kwakwalwa

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Attajirin fasaha a duniya Elon Musk ya ce kamfaninsa na Neuralink ya samu nasarar dasa na’urar da za ta yi aiki a kwakwalwar dan Adam a karon farko.

    Ana fatan za ta yi aiki da kwakwalwa domin ba mutanen da suka samu mutuwar sashen jiki damar iya sarrafa na'ura da tunaninsu.

    A bayanin da ya wallafa a shafinsa na X, Elon Musk ya ce wanda aka yi wa gwajin na’urar rahotanni na cewa yana murmurewa sosai daga aikin dashen da aka yi ranar Lahadi – kuma sakamakon farko ya nuna akwai nasara.

    Kamfanin mista Musk dai na ƙoƙarin ƙirƙirar wata sabuwar fasahar da za ta samar da sadarwa kai tsaye tsakanin kwamfuta da kwakwalwar ɗan’adam – da nufin samun mafita ga kalubalen da suka shafi kwakwalwa da likitoci ke fuskanta.

    Wadannan sun hada da mutuwar sashen jiki da makanta da tsananin ciwon damuwa da suka shafi kwakwalwa.

    Kamfanin Musk dai ba shi ne na farko da ya fara aikin samar da fasahar ba akwai wasu kamfanoni da tuni suka yi irin wannan dashen amma kasancewar mista Musk fitacce ne hakan zai yi tasiri ga kamfaninsa na Neuralink da ke aikin fasahar.

    • Elon Musk ya kafa tarihi bayan arzikinsa ya ragu
    • Elon Musk na fuskantar shari'a kan sakon da ya janyo wa masu hannun jarin Tesla asarar biliyoyin dala
  6. 'Mutum fiye da 20 sun mutu a wani hari da aka kai Nijar'

    Akalla mutum 22 aka kashe a wani hari da ake tunanin na masu ikirarin Jihadi ne a wani kauye da ke Nijar kusa da iyakar kasar da Mali, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

    Wani jami'i a yankin ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa a ranar Lahadi ne maharan suka isa kauyen Motagatta a yankin Tillaberi kan babura inda suka bude wa jama'a wuta.

    Babu masaniya kan wadanda ke da hannu a kai harin sannan sojojin da ke mulki a Nijar ba su ce komai ba a kan harin.

    Amma dai an sha ganin afkuwar ire-iren wadan nan hare-hare da ke janyo asarar rayuka a Nijar inda rikicin masu ikirarin Jihadi ke karuwa tun 2015.

    Kusan sojoji 40 aka kashe a bara a wasu hare-hare da aka kai kusa da iyakar kasar da Burkina Faso.

    Sojojin da suka kifar da gwamnati a kasar cikin shekarar da ta gabata sun ce sun dauki matakin ne ganin yadda tsaro ya tabarbare a kasar.

    A watan Disamba ne, mutumin da ya jagoranci hambarar da gwamnati, Janar Abdourahamane Tiani ya ce al'amura sun fara daidaita bayan abin da ya kira jerin nasarorin da sojoji suka samu wajen yayyafawa tashin hankalin ruwa. Sai dai hare-haren sun ci gaba.

    Sojojin Faransa sun fice daga Nijar bayan da sojojin da ke mulki a kasar suka umarce su da su bar kasar.

    • An kai wa shalkwatar PNDS hari bayan hamɓaras da Bazoum
    • Rikicin Filato: 'Na ga gawawwaki yashe a kan titi'
  7. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyarmu, Barkanmu da war haka, da fatan muna cikin ƙoshin lafiya.

    Kamar kullum, a yau ma wannan shafi na Kai Tsaye zai kawo rahotanni da labarai na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sauran kasashe makwabta.

    Sai ku ci gaba da bibiyar mu domin sanin halin da duniya take ciki a yau Talata.

    Kuna kuma iya lekawa shafukanmu na sada zumunta domin karanta karin labarai da kallon bidiyo.