Kotun Kenya ta dakatar da shirin gwamanti na karɓar harajin gidaje

Asalin hoton, Reuters
Wata kotu a Kenya ta dakatar da shirin gwamnatin kasar na karɓar harajin gidaje daga al'umma, har sai an saurari karar da ake yi kan lamarin da kuma yanke hukunci.
Babbar Kotun ta gano cewa harajin ba bisa ka'ida ba ya shafi 'yan kasar Kenya da ke aiki a fannin ma'aikatun gwamnati.
Tun a watan Yulin shekarar da ta gabata ne gwamnati ta fara cire kashi 1.5% na yawan albashin ‘yan ƙasar da kuma na ƙasashen waje, domin gina gidaje masu rahusa ga masu karamin karfi.
Matakin harajin dai ya janyo ce-ce-ku-ce daga ɓangaren 'yan adawa da kuma wani ɓangare na al'umar da dama, wadanda ke ganin rashin dacewar ɓullo da harajin a karkashin Shugaba William Ruto.
Gwamnati ta yi zargin cewa dakatar da harajin zai jefa dubban ma'aikata a karkashin shirin gina gidaje cikin rashin aikin yi da kuma karya kwangilolin da aka riga aka sanya wa hannu.
Shari’ar dai na daga cikin kararrakin da suka haifar da rashin jituwa tsakanin bangaren shari’a da zartarwa, inda shugaba Ruto ya zargi alƙalan da cin hanci da rashawa da hada baki da ‘yan adawa wajen yin zagon kasa ga ayyukan ci gaban kasa.










