Rufewa
Masu bin shafin BBC Hausa Kai-tsaye nan muka kawo ƙarshen labarai da rahotonnin.
Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu, za mu sake dawowa da wasu sabbin labaran.
Abdullahi Bello Diginza ke cewa mu kwana lafiya
Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Wannan shafi ne da ke kawo muku bubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.
Nabeela Mukhtar Uba, Haruna Kakangi, A'isha Babangida and Abdullahi Bello Diginza
Masu bin shafin BBC Hausa Kai-tsaye nan muka kawo ƙarshen labarai da rahotonnin.
Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu, za mu sake dawowa da wasu sabbin labaran.
Abdullahi Bello Diginza ke cewa mu kwana lafiya
Jagoran adawar Zimbabwe, Nelson Chamisa, ya ce ya fice daga ƙawancen adawar da ya kafa shekara biyu da suka wuce bayan ya yi zargin cewa jam'iyya mai mulki na yi ƙawancen kutse.
A watannin baya-bayan nan ƙawancen raajin kawowa 'yan ƙasar sauyi ya sabu rarrabuwar kawuna, inda ake ta samun matsaloli a ƙawancen bayan aka ayyana fiye da kujeru 30 da ƙawance ya samu a matsayin waɗanda babu ma su su, wani lamari da ya janyo ce-ce-ku-ce.
Nelson Chamisa ya ce ƙawancen da ya kafan ya cakuɗa da abubuwa masu yawa, kuma jam'iyyar mai mulki ta maƙure shi.
A yanzu ana sa ran zai kafa wata sabuwar jam'iyya.
Mista Chamisa ya samu kashi 44 na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen shugaban ƙasara na shekarar da ta gabata.
Wata babbar kotu a jihar Kano ta yanke wa wasu `yan banga biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan ta kama su da laifin kisan wani matashi mai shekara 17.
'Yan bangar sun aikata laifin ne a ranar 22 ga watan Janairun 2022.
'Yan bangar, waɗanda suke aiki a cibiyar bunƙasa rayuwar matasa ta Sani Abacha da ke kan hanyar Madobi, sun haɗa da Emmanuel Korau da Elisha Ayuba da Irimiya Timothy da Auwalu Jafar da kuma Mustapha Haladu.
Lauyan da ya gabatar da kara Barrister Lamido Soron Dinki, gabannin yanke hukuncin ya shaida wa kotun cewa waɗanda ake zargi sun kama matashin ne a sabon titi, Panshekara, inda suka far masa da duka da da sanduna, kana daga bisani suka raunata shi ta hanyar caka masa wuka, kana suka ja shi a kasa suka jefa shi cikin keken a daidaita sahu, lamarin da ya yai sanadin mutuwarsa.
Lauyan waɗanda aka yi ƙarar ya yi ƙokarin kare su, inda ya bayyana cewa sun je ne da nufin kama matashin ba halaka shi ba, bayan an kai musu karan sa.
Sai dai, kamar yadda mai magana da yawun kotunan jihar Kano, Malam Baba Jibo Ibrahim ya ce, mai shara`a Dije Aboki ta yanke wa `yan bangan hukunci ne bayan ta gamsu da hujjojin da mai gabatar da ƙarar ya gabatar:
Sai dai kuma mutanen da aka yanke wa hukuncin na da damar ɗaukaka ƙara.
Jagoran adawar Najeriya Atiku Abubakar ya ce ya kamata gwamnatin shugaba Tinubu ta fito ta yi wa 'yan Najeriya bayani kan bashin dala biliyan 3.3 da kamfanin mai na ƙasar NNPC ta ciyo da nufin farfaɗo da darajar kudin ƙasar.
A shekarar da ta gabata ne Kamfanin mai na ƙasar NNPC ciyo bashin domin taimakawa wajen farfaɗo da darajar naira a kasuwar musayar kuɗaɗe.
To sai dai a cikin wata sanarwar da tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya fitar, ya ce wani abin mamaki shi ne har yanzu gwamnati ba ta ce komai ba game da lamarin, kuma bayanan kawai da ake samu kan batun, ana samun su ne ta wasu majiyoyin da ba na hukuma ba daga kamfanin.
''An ƙulla yarjejeniyar ce da nufin biyan kuɗin da man fetur, wanda aka ƙulla da bankin ''African Export-Import'' kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Atiku Abubakar ya ce abin da suka gano shi ne a yanzu Najeriya na haƙo gangar mai miliyan 1.38 a kowace rana, kuma daga cikin ƙa'idojin yarjejeniyar bashin akwai batun cewa Najeriya za ta riƙa bayar da ganga 90,000 a kowace rana da nufin biyan bashin, daga 2024 har zuwa ganga miliyan 164.25 da za a kammala biyan bashin da shi.
''To a nan ne matsalar take, domin kuwa abin da Najeriya ta tsara za ta riƙa sayar da kowace gangar mai a shekarar 2024 shi ne dala 77.96'', in ji Atiku.
''Ka ga idan aka lissafa wannan kuɗi da miliyan 164.25, kuɗin zai kama dala biliyan 12, a kan wannan ne muke son gwamnati ta fito ta yi mana bayanin yadda yarjejeniyar take'', in ji jagoran adawar ƙasar.
Sanarwar ta ce abu ne da hankali ba zai iya ɗauka ba, a ce gwamnatin tarayya za ta karɓo bashin dala biliyan 3.3 da kuɗin ruwa na kashi 12, amma ƙiyasin abin da za a biya a ce ya kai dala biliyan 12.
Wannan na nufin cewa an samu bambancin dala biliyan bakwai tsakanin abin da ke rubuce a takarda da abin da yake a zahiri.
Atiku Abubakar ya ce akwai tambayoyin da 'yan ƙasar ke buƙatar sanin amsarsu game da yarjejeniyar, kan haka ne muke buƙatar gwamnatin tarayya ta fito ƙarara ta yi bayaninsu.
''Don haka muke kira a madadin 'yan Najeriya, gwamnatin tarayya ta amsa mana waɗanna tambayoyi''.
1. Shin gwamnatin tarayya ce ta ƙarbo bashin?
2. Shin bashin na daga cikin basussukan da majalisa ta amince wa gwamnati?
3. Su wane ne a cikin yarjejeniyar bashin, kuma wace rawa za su taka a yarjejeniyar?
4. Waɗanne ne ƙa'idojin bashin, ciki har da wanda ya ciwo shi, da yadda za a biya, da kadarar da aka ajiye don ƙulla yarjejeniyar, da kuma kuɗin ruwa?
5. Daga ƙarshe, kuma me ya sa wani kamfanin Bahamas ke cikin yarjejeniyar?
A wani samame da rundunar yaki da garkuwa da jama'a ta 'yan sandan birnin tarayyar Najeriya, Abuja da ke garin Rubochi na karamar hukumar Kuje ta aiwatar a kauyen Ukya da ke kan iyaka da jihar Nassarawa ta samu nasarar tseratar da wadanda masu garkuwa suka sace su 14.
Wata sanarwa da rundunar 'yan sandan birnin tarayya ta fitar, rundunar ta ce sun samu nasarar ceto mutanen ne bayan kaddamar wa wurin da masu satar jama'a suke, inda kuma masu garkuwar da jama'a suka fara da bude wa 'yan sanda wuta.
To sai dai 'yan sandan sun ce hakan ne ya sa jami'ansu suka mayar da wutar abin da ya yi sanadiyyar kashe mai garkuwar guda daya sannan sauran suka ranta a na kare tare da raunukan harbi a jikinsu.
Amurka da Birtaniya sun bayyana ƙaƙaba wa wasu manyan jami'an ƙungiyar Houthi huɗu a Yemen takunkumi, a wani mataki na yunkurin dakatar da hare-haren da ƙungiyar ke kai wa jiragen ruwa a tekun Maliya.
Ƙasashen biyu na kallon mayakan a matsayin masu shirya hare-hare kan jiragen, lamarin da ke kawo cikas ga jigilar jiragen ruwa a yankin
Sakataren harkokin wajen Birtaniya David Cameron ya ce takunkuman wani saƙon gargaɗi ne ga hare-haren ƙungiyar na baya-bayan nan.
Yana mai cewa Birtaniya tare da ƙawayenta za su ci gaba da daukar mataki kan waɗanda ke shirya haramtattun hare-haren da ba za a lamunta ba, da ƙungiyar Houthi ke jagoranta a tekun Maliya.
''Hare-hare ne da ke barazana ga rayukan mutanen da ba su ji ba su gani da da kuma mutanen Yeman'', in ji Cameron.
Ministan yada labarai da wayar da kai na Najeriya, Alhaji Muhammad Idris Malagi ya bukaci shugabannin hukumomi masu watsa labarai da kafafen watsa labarai na kasar da su kyautata aikinsu ta hanyar amfani da sabon ma'aunin fahimtar hallayar masu hulda da kafafen watsa labarai musamman rediyo da talbijin na kasar.
Ministan dai na wannan bayani ne a lokacin kaddamar da wannan sabon mizani wanda kwararru da masana suka kwashe dogon lokaci suna bincike kuma suka mika shi ga gwamnatin tarayya.
Mizanin mai shafi 182 wanda zai maye gurbin tsohon tsarin ya mayar da hankali ne kan yawan mutanen da suke mu'amila da kafafen watsa labaran kasar.
Ministan ya yi kira ga shugabannin gidajen watsa labarai da hukumar tallace-tallace da su ci moriyar tsarin ta hanyar sanin hakikanin mutanen da ke mu'amila da su, inda kuma hakan zai ba su kudin shiga.
A Jamhuriyar Nijar tattaunawar da aka shirya yi tsakanin hukumomin milkin sojin ƙasar da ƙungiyar Raya tattalin arzikin Yammacin Afirka, ta Ecowas ta ci tura.
Hukumomin ƙasar sun ɗora alhakin hakan kan ƙungiyar ta Ecowas - wadda jagororin mulkin sojin suka ce - ta ƙi amsa goron gayyatar.
Yayin wani taron manema labaran da ya kira a fadarsa, Firaministan ƙasar, Ali Lamine Zeine ya bayyana abin da Ecowas ta yi a matsayin rashin adalci.
Daga Yamai ga rahoton Tchima Illa Issoufou
Jami'ai a Mali sun ce aƙalla mutum 40 ne suka mutu bayan wata mahaƙar Zinari ta rufta a ƙasar.
Wani jami'in haƙar ma'adinan, mai suna Oumar Sidibe ya shaida wa kamfanin dilancin labarai na AFP cewa, an fara jin ƙara a mahaƙar kafin ƙasa ta fara girgiza''.
Mahaƙar ta rufta ne a yankin Koulikoro da ke kudu maso yammacin ƙasar a makon da ya gabata, amma ba a bayar da rahoton adadin mutanen da suka mutun ba.
Mai magana da yawun ma'aitakar ma'adinan ƙasar Baye Coulibaly ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa waɗanda suka mutum sun zarta mutum 40.
To amma kamfanin dillancin labarai na AFP ya ambato wani jami'i yana cewa, fiye da mutum 70 ne suka mutu.
Mista Sidibe ya ce: "Akwai fiye da mutum 200 da ke haƙar zinaren a mahaƙar lokacin da abin ya faru, kuma a yanzu an kammala aikin ceton, inda aka tabbatar da mutuwar mutum 73.
Gwamnatin Mali ta buƙaci mutanen da ke zaune a kusa da wuraren haƙar ma'adinai da su riƙa biyayya ga ƙa'idojin kariya.
Ruftawar mahaƙar ma'adinai ba sabon abu ba ne a Mali, inda masu haƙar ma'adinan ba bisa ƙa'ida ba ke amfani da hanyoyin da ba su dace ba wajen haƙo ma'adinan.
Kamfanin 'Time Out' da ke lura da ƙididdigar daɗin zama a biranen duniya ya ce birnin Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya ne birni na 19 mafi daɗin ziyarta a duniya.
Kamfanin ya wallafa jadawalin birane 50 da ya ce sun fi daɗin zama daga cikin fiye da birane 20,000 da ya gudanar da bincike a kansu a faɗin duniya.
Birnin New York na Amurka ya kasance birni na farko mafi daɗin ziyarta a duniya, daga nan sai birnin Cape Town na Afirka da Kudu a matsayi na biyu da birnin Berlin na Jamus a matsayi cikin birane 50 na duniya.
Kamfanin ya yi amfani da wasu ƙa'idoji wajen fitar da jawadalin inda suka haɗar da ingancin abinci da kuma sauƙinsa da al'adu da rayuwar cikin dare da ake yi a birni.
Sauran ka'idojin su ne yadda mazauna birnin ke ji da shi da irin manyan mutanen da ke rayuwa a birni, da wuraren shaƙatawa da na tarihi da sauran abubuwa.
Kamfanin ya ce Legas birni ne da kowa zai iya ziyarta ''da wanda ya saba rayuwa a tsibiri da wanda ya saba rayuwa a kan tudu, kowa zai ji daɗin birnin Legas, wanda shi ne birnin da ya fi kowanne mutane a nahiyar Afirka''.
Biranen London da Madrid sun kasance a matsayi na huɗu da na biyar, sai biranen Mexico City da Liverpool da kuma Tokyo da Rome da kuma Porto ke biye musu.
Kasar Qatar ta ce ba ta ji dadin kalaman da aka alakanta wa firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ba, inda aka ce ya bayyana irin rawar da Qatar din ke takawa a samar da sulhu a yakin Gaza da "matsala".
Gidan talbijin na Isra'ila ta watsa abin da ta ce kalaman Netanyahu ne da aka nada inda yake shaida wa iyalan wadanda kungiyar Hamas ta yi garkuwa da su cewa "ba ku ji ni ina yaba wa Qatar ba".
"Suna bukata.....domin su ne suke mara wa Hamas baya," kamar ya kara.
Qatar ta ce kalaman na Netanyahu, idan dai gaskiya ne to "na rashin tunani ne" amma "ba su zo mata da ba zata ba".
Kasar dai ta Qatar ta kasance mai alaka da kasar Isra'ila tun shekarun 1990, to sai dai ba su taba tabbatar da hakan a hukumance ba.
An dai san kasar ta Qatar da yin uwa da makarbiya wajen tallafa wa al'amuran Falasdinawa sannan kuma ita ce mai masaukin jagororin kungiyar Hamas wadda Isra'ila da Burtaniya da Amurka suka ayyana a matsayin kungiyar ta'addanci.
Sakataren harkokin wajen Birtaniya, David Cameron ya yi kiran a gaggauta tsagaita wuta a Gaza domin samun damar kai wa jama'a ɗauki da kuma ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.
Da ya ke jawabi a birnin Doha, Mr Cameron ya ce yana fatan a tsagaita wuta ba da bata lokaci ba.
Ya kara da cewa "yana da muhimmancin gaske su bayar da biza ga ma'aikatan Majalisar Dinkin Duniya domin kai tallafi ga jama'ar Gaza".
Mr Cameron ya kuma buƙaci Isra'ila ta gaggauta bayar da damar shigar da kayan agaji Gaza ba tare da wata tangarɗa ba.
Hukumar ƙididdiga ta Najeriya, NBS ta ce an samu ƙari a farashin shinkafa a ƙasar a shekarar 2023.
NBS ta ce farashin kilogiram ɗaya na shinkafa 'yar gida ya ƙaru da naira 411.76 idan aka kwatanta da 506 da aka sayar da ita a watan Disamban 2022.
Cikin rahoton farashin wasu kayyaki a watan Disamban 2023, da hukumar ta fitar ranar Laraba ya nuna cewwa matsakaicin farashin kilo guda na shinkafar gida a watan Disamban 2023 shi ne naira 917.93.
“Hakan na nufin an samu tashin farashin da kashi 81.35 cikin 100 cikin shekara guda, wato daga naira 506.17 a watan Disamban 2022 zuwa naira 867.18 a watan Nuwamban 2023'', in ji rahoton.
Sai dai manoman shinkafan sun ce ba su mamakin tashin farashin ba, idan aka yi la'akari da tsadar taki da sauran kayayyakin noma da suka fuskanta.
Shugaban ƙungiyar Manoman shinkafa na jihar Jigawa, Alhaji Adamu Maigoro Haruna ya shaida wa BBC cewa a daminar da ta gabatan an samu ƙarancin zubar ruwan sama, haka kuma masu bayi ta hanyar amfani da ruwan koguna, to kogunan ba su da ruwa, suma masu amfani da inji sun fuskancin tsadar man fetur da za su yi amfani da shi wajen tayar da injunan bayi.
''Hakan ya sa aka samu ƙarancin shinkafar a daminar da ta gabata, domin wanda ke tsammanin zai samu buhu 100 dakyar ya samu 20 ko 30'', in ji shi.
Rahoton NBS din ya kuma nuna cewa matsakacin farashin kilo ɗaya na tumaturi ya ƙaru da kashi 77.60 cikin shekara guda, sannan farashin wake ya karu da kashi 48.54, sai farashin jan nama da ya ƙaru da kashi 32.38.
Ministan ma'aidan Kenya Salim Mvurya ta ce ƙasar ta gano ajiyayyen ma'adinin colton da ake amfani da shi wajen ƙera manyan wayoyin hannu da sauran kayan laturoni a karon farko a ƙasar.
Ba kasafai aka fiya ganin ma'adinin mai daraja ba, wanda ake amfani da shi wajen yin batirin mota mai amfani da wutar lantarki da wayoyi da sauran kayan laturoli.
Jamhuriyar Damokaraɗiyyar Congo ce ke da fiye da kashi 70 na ma'ajiyar ma'adanan coltan a faɗin duniya, wanda a gomman shekaru ya yi sanadiyyar tashin rikici a ɓangaren gabashin ƙasar.
Har yanzu ba'a tabbatar da yawan ma'dinin da aka gano a Kenya ba.
A baya dai jami'an haƙar ma'adanai sun ce akwai yiwuwar samun ma'adanai masu daraja a Kenya.
Sai dai a ranar Talata ministan haƙar ma'adanai da arziƙin cikin ruwa na Kenya, Salim Mvurya ya ce "yanzu an tabbatar a hukumance" cewa Kenya na da ma'adanin Coltan.
An samu ma'adinin a ƙananan hukumomi shida da ke sassan ƙasar ,amma har yanzu ba a ƙimanta darajarsu ba.
"Za mu bar wa tawagarmu alhakin yin bincike da samun sahihan bayanai kan yadda za mu iya ƙiyasta darajarsa a kasuwanni'', in ji Mista Mvurya.
An shawarci mazauna ƙaramar hukumar Embu da ke gabashin Kenya da su riƙe ƙasarsu da kyau kasancewarta ɗaya daga cikin kananan hukumomi shida da aka samu ma'adanin a ciki.
Wani Alkalin ƙasar Sifaniya ya ce ya kamata tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar Luis Rubiales ya gurfana a gaban kotu kan sumbatar da ya yi wa kyaftin ɗin tawagar ƙwallon ƙafar matan ƙasar, Jenni Hermoso a gasar cin kofin duniya.
Mista Rubiales ya kama kan Ms Hermoso kuma ya sumbace ta yayin gabatar da jawabi bayan nasarar da Sifaniya ta samu a Australia.
Ta ce sumbatar "ba da amincewarta ba ne", iƙirarin da Mista Rubiales ya musanta.
Alkalin ya ce ya gano wasu isassun shaidun da za su iya bayar da damar ci gaba da shari’a.
A yayin sauraren ƙarar da aka yi a Madrid, alƙalin ya bayyana sumbatar a matsayin "ba ba da amincewar juna ba kuma wani shiri ne mai ban mamaki", a cewar wata sanarwa da kotun ta aike wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
A baya dai masu gabatar da ƙara sun tuhumi Mista Rubiales da laifin yin lalata da kuma tilastawa.
Hukunce-hukuncen irin wannan sumbatar ya haɗu da tara da kuma shekara hudu a gidan yari.
Lamarin dai ya shafi shugabannin hukumar kwallon kafar Sifaniya da dama da suka hada da tsohon kocin Hermoso da tsohon manajan tallace-tallace da kuma daraktan wasanni na ƙungiyar maza.
Ana zargin Jorge Vilda, da Rubén Rivera da Albert Luque da tursasa Ms Hermoso wajen faɗin cewa da amincewarta ya sumbace ta.
Alkalin da ke birnin Madrid ya ce ya kamata su ma 'yan wasan uku su gurfana gaban kotu.
Rundunar sojin Najeriya sun musanta zargin nuna son kai da ake yi musu a rikin ƙaramar hukumar Mangu na jihar Plateau.
Cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron ƙasar ta fitar, mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaran rundunar Birgediya Janar Tukur Gusau, ya ce bidiyon da shugaban ƙungiyar Kiristocin Najeriya CAN, Reverend Timothy Daluk, ya yi, da ke zargin jami'an sojin da ake aiki domin kwantar da rikicin da ya ɓarke a yankin na nuna son kai.
Sanarwar ta ce zarge-zargen da ke cikin bidiyon na ce sojojin na goyon bayan wani ɓangare a rikicin, ba su ta tushe balle makama.
A ranar 23 ga watan Janairu ne wani rikici ya ɓarke a ƙaramar hukumar Mangu da ke jihar, lamarin da ya sa gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita ta tsawon kwana guda.
An kuma tura jami'an soji da ke aiki da rundunar Operation SAFE HAVEN mai yaƙi da 'yan bindiga zuwa yankin domin tabbatar da bin dokar tare da maido da kwanciyar hankali da kuma daƙile bazuwar rikicin zuwa wasu sassan jihar.
Birgediya Tukur Gusau ya ce dakarun sun gudanar da ayyukansu yadda ya kamata cikin ƙwarewa da bin tsarin doka, Inda suka samu nasarar kama wasu daga cikin waɗanda ke da hannu a rikicin da ya yi sanadin ɓarna da ƙona dukiyoyi tare da da ƙwato makamai.
"Amma abin takaicin shugaban addini, wanda ake tunanin zai nuna halin gaskiya da adalci wajen hana bazuwar ƙarairayi kan sojoji'', in ji Janar Gusau.
Ya ƙara da cewa "Muna son jaddada cewa sojoji ba sa ɗaukar ɓangaranci, kuma suna mayar da hankali wajen gudanar da aikinsu kamar yadda kundin tsaron mulki ya tanadar na kare rayuka da dukiyoyin 'yan ƙasa, za mu ladabtar da duk wanda aka samu da saɓa dokar ƙasa ba tare da son rai ko ɓangaranci ba''.
Daga ƙarshe ya gargaɗi duka 'yan ƙasar da ke yi wa sojoji irin waɗanna zarge-zarge da su daina, ko su ɗanɗana kuɗarsu duk kuwa da irin matsayin da suke da shi a cikin al'umma.
Ya ce irin waɗanna zarge-zarge ba za su sanyaya musu giwwa ba a ƙoƙarin da suke yi na kawar da duka nau'ikan fitintinu a faɗin ƙasar.
Ya kuma yi kira da 'yan ƙasar da su ci gaba da mara wa sojojin ƙasar baya a ƙoƙarinsu na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
An yanke wa wata ‘yar ƙasar Rasha Darya Trepova hukuncin daurin shekaru 27 a gidan yari, sakamakon kisan da ta yi wa wani Vladlen Tatarsky, mai goyon bayan yaƙi a watan Afrilun da ya gabata.
Ta kashe Tatarsky ta hanyar bam a cikin wani mutum-mutumi da Ta ba shi, a lokacin da yake shirin yin jawabi a St Petersburg.
Mutane da dama ne suka jikkata sakamakon fashewar bam din.
Trepova, mai shekaru 26, ta musanta tuhumar da ake mata, tana mai cewa tana tunanin mutum-mutumin na dauke da na'urar saurare.
Ta ce ta yi aiki da umarnin wani ɗan ƙasar Ukraine, kuma an kafa mata tarko ne.
Hukuncin na ɗaya daga cikin hukunci mafi tsauri da aka yankewa wata mace a tarihin kasar Rasha.
An dai kai wai Tatarsky, mai shekaru 40 harin ne a ranar 2 ga Afrilu, 2023.
An tuhumi Trepova da "aikin ta'addanci da wata kungiya ta shirya wanda ya haddasa kisa da gangan" da kuma "mallakar abubuwan fashewa ta wata kungiya ba bisa ka'ida ba".
Masu bincike na Rasha sun zargi Ukraine da kai harin, kuma jami'an Ukraine ba su tabbatar ko musanta hakan ba.
'Yan sanda a kasar Thailand sun kama wata mata da aka dauki hoton zakin da ta mallaka ta ajiye a gidanta yana yawo a cikin mota a titunan Pattaya.
Bidiyon da a yanzu ya fara yaɗuwa ya nuna ɗan zaki mai ɗaure a sarka yana zaune a bayan wani farin mota.
Wani dan kasar Sri Lanka ne ke tuƙa zakin wanda a hanlin yanzu ya bar kasar, kuma ana kyautata zaton abokin matar mai zakin ne, Sawangjit Kosoongnern.
Duk da cewa mallakar zaki a Thailand ba bisa ka'ida bane, hakan na buƙatar a yi masa rajista a hukumance.
Hukumomi a Thailand sun ce Sawangjit ta yi ikirarin cewa ta sayi dabbar daga hannun wani dan ƙasar Thailand a lardin Nakhon Pathom, wanda ya yi nasarar kai zakin zuwa Pattaya.
Sai dai ya gaza wajen samun jami’ai su duba kafin ya siyar da zakin, lamarin da ya sanya mallakar dabbar haramtacciya.
Don haka tana fuskantar tuhumar mallakar dabbar dawa ba tare da izini ba, wanda ke da hukuncin daurin shekara guda a gidan yari da tarar baht 100,000 kwatankwacin dalar Amurka 2,800 kenan.