Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni daga sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Habiba Adamu, Nabeela Mukhtar Uba, Haruna Kakangi, Mukhtari Adamu Bawa and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Zambiya za ta karɓi kashin farko na rigakafin kwalara da ta ɓarke a ƙasar

    ..

    Asalin hoton, Zambia Presidency/Facebook

    Zambiya na shirin karɓar alluran rigakafin cutar kwalara miliyan 1.6 yayin da ƙasar ke fama da ɓarkewar cutar mafi muni.

    Fiye da mutum 350 sun mutu sannan mutum 9,000 suna fama da cutar tun lokacin da ta ɓarke a watan Oktoban bara.

    Gwamnatin Zambiya ta samo alluran da haɗin gwiwar Hukumar Lafiya ta Duniya da hukumar kula da kananan yara ta Majalisar Dinkin Duniya, Unicef.

    Ma'aikatar lafiyar ƙasar ce za ta karɓi alluran a hukumance bayan an shigar da su ƙasar da yammacin jiya Lahadi.

    "Bayan nan kuma ma'aikatar za ta kammala shirye-shirye na soma yi wa al'umma rigakafin a zaɓaɓun cibiyoyi a Lardin Lusaka," in ji ma'aikatar lafiyar inda ta ce Lardin ne aka fi samun masu fama da cutar ta kwalara.

    A yanzu cutar ta bazu zuwa Larduna tara cikin 10 na ƙasar ta Zambiya.

    Hukumomin ƙasar sun ɗauki matakan kariya daban-daban domin daƙile yaɗuwar cutar ciki har da jinkirta komawar ɗalibai makaranta da taƙaita masu zuwa jana'izar mutanen da cutar ta halaka zuwa mutum biyar.

    Filin wasa mafi girma da ke ƙasar a yanzu hukumomi sun mayar da shi wajen kula da masu cutar ta kwalara.

    Gwamnati ta kuma yi kira ga al'ummar ƙasar da ke zaune a birni su koma ƙauyuka.

  2. Mutumin da ake zargi da ƙwacen waya a Kano ya gamu da ibtila'i

    ..

    Asalin hoton, Abdullahi Haruna Kiyawa/Facebook

    Rundunar ƴan sandan Najeriya reshen jihar Kano ta ce wani mutum da ake zargi da ƙwacen waya yana cikin mawuyacin hali bayan da mota ta buge shi a lokacin da yake ƙoƙarin tsallaka titi sa'ilin da ya yi yunƙurin tserewa bayan yin ƙwacen waya.

    Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya tabbatar da hakan a shafinsa na Facebook inda ya ce lamarin ya rutsa da shi ne yayin da yake ƙoƙarin guduwa bayan ya ƙwace wayar wata mata ta hanyar yi mata barazana da makami.

    SP Kiyawa ya bayyana cewa sun garzaya da mutumin asibiti inda kuma ya ce ya samu matsalar laka sannan kuma "kansa ya fashe".

    Ƙwacen waya matsala ce da ta yi ƙamari a wasu jihohin Najeriya kuma hukumomin tsaro sun sha bayyana ƙoƙarin da suke na daƙile ta.

  3. Yawan Falasɗinawan da aka kashe a Gaza ya zarce 24, 000

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Ma'aikatar lafiya ta Hamas da ke Gaza ta wallafa sabuwar ƙididdigar mutanen da suka mutu a Zirin tun bayan ɓarkewar yaƙi.

    Aƙalla mutum 24,100 ne aka tabbatar da mutuwarsu, a cewar ta. Ta ƙara da cewa fiye da mutum 100 aka kashe cikin sa'a 24 da ta gabata.

    Sashen BBC Verify da ke tabbatar da sahihancin labarai a baya ya duba yadda ake ƙirga mutanen da suka mutu a Gaza.

    Yaƙi ya ɓarke ranar 7 ga watan Oktoba bayan da Hamas ta kai hari kan Isra'ila tare da kashe mutum 1,200 da garkuwa da ɗaruruwa.

    Tun lokacin kuma Isra'ila take kai hare-hare ba ƙaƙƙautawa a wani mataki na martani - ban da tsagaitar wutar da aka samu na tsawon mako ɗaya.

  4. Zaftarewar ƙasa ta binne masu haƙar ma'adanai 22 a Tanzania

    Kasashen nahiyar Afrika na fama da matsalar haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Kasashen nahiyar Afrika na fama da matsalar haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba

    Mutane 22 sun rasa rayukansu a zaftarewar ƙasa da aka samu a wani wurin haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba a arewacin Tanzania, a cewar jami'ai.

    Lamarin ya auku ne a mahaƙar Ng'alita da ke gundumar Bariadi, a yankin Simiyu a ƙarshen mako, Inji kwamishinan gundumar, Simon Simalenga.

    Iftila'in ya auku ne bayan wasu mutane sun fara haƙar ma'adanai a wani wuri da aka haramta haƙar ma'adanai saboda ruwan sama kamar da baƙin ƙwarya, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

    Shugabar ƙasar, Samia Suluhu ta bayyana matuƙar rashin jin daƙinta kan lamarin.

    "Waɗannan ƴan ƙasata ta Tanzania ƙananan masu haƙar ma'adanai ne da ke neman abin sa wa a bakin salatinsu da kula da iyalansu," Ta bayyana hakan a shafinta na X.

    Mr Simalenga ya ce da fari an ce masa mutane 19 zuwa 20 ƙasar ta binne a mahaƙar, amma an zaƙulo gawawwaki 22.

    An sanar da kammala ayyukan neman gawawwaki saboda an yi amanna babu sauran da suka rage.

    Mr Simalenga ya ce mutanen sun fara aiki ne a wurin mako uku gabannin gwamnati ta ƙaddamar da wasu tsare-tsare na kiyayewa.

    "An kuma je an dakatar da su saboda ana aiki a kan tsare-tsaren da ake buƙatar aiwatarwa a wurin." In ji Mr Simalenga.

    Ayyukan haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba lamari ne da ya zama ruwan dare a Tanzania, wadda ita ce ƙasar da ta fi kowacce samar da zinare a duniya.

  5. Sakamakon wasannin Afcon 2023

  6. Matatar Dangote ta yi rajistar dilolin da za su raba mai a Najeriya

    ..

    Asalin hoton, PRESIDENCY

    Manyan ƴan kasuwa masu hada-hadar mai guda bakwai a Najeriya sun yi rajista da katafariyar matatar mai ta Aliko Dangote domin ɗaukar mai da kuma rarraba shi da dangoginsa a ƙasar.

    Dilolin a ƙarkashin wata ƙungiya ta manyan ƴan kasuwa masu hada-hadar mai sun tabbatar da hakan a ranar Lahadi.

    Haka kuma sun ce za su fara rarraba mai daga matatar, da zarar an kammala yarjejeniyar kasuwanci.

    Hakan na zuwa ne a yayin da ita ma ƙungiyar 'yan kasuwa masu zaman kansu ta bayyana cewa za ta gana da hukumar gudanarwa ta matatar a wannan makon don tattauna batun ɗaukar man.

    Ita ma kungiyar masu sarin mai ta Najeriya, PETROAN tana tattaunawa da matatar don samar da mai daga matatar.

    A ranar Juma'a ne matatar man ta Dangote ta sanar da fara sarrafa man dizel da man JetA1 na jiragen sama.

    • Matatar man Dangote ta karɓi ɗanyen man fetur a karon farko
    • Ko sabuwar matatar man Dangote za ta magance matsalar man fetur a Najeriya?
  7. Bidiyon girman ɓarnar da aka yi a Gaza bayan kwana 100 da yaƙi

    Bayanan bidiyo, Bidiyon yadda Gaza ta kasance bayan kwana 100 da yaƙi

    Isra'ila ta ce ta yi amfani da fiye da bama-bamai da makamai masu linzami 10,000 tare da ƙaddamar da ɗaruruwan hare-hare a sassan Gaza tun 7 ga watan Oktoba bayan da ƙungiyar Hamas ta kai hari kan Isra'ila.

    Hukumomi a Gaza sun ce an lalata fiye da kashi 50 cikin 100 na rukunin gidaje a Gaza tun soma yaƙin.

    An ba da rahoton tserewar kusan mutum miliyan biyu a zirin - kashi 85 cikin 100 daga gidajensu.

    Jirage marasa matuƙi masu ɗaukar hotuna sun nuna girman ɓarnar da yaƙi ya yi a Khan Younis da Maghazi da Rafah.

    • An faɗa wa kotu jami'an gwamnatin Isra'ila na goyon bayan a ruguza Gaza
    • Dole a bar Falasɗinawa su zauna a Gaza - Blinken
  8. Mahaukaciyar guguwa ta sa an rufe makarantu a Mauritius, Daga Yasine Mohabuth a babban birnin Mauritius, Louis

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, An gargadi mutane da su zauna a gida

    An rufe makarantu a tsibirin Mauritius bayan hasashen samun mamakon ruwan sama da zai iya janyo ambaliyar ruwa.

    An sanya tsibirin Réunion wanda ba shi da nisa, a cikin halin ko-ta- kwana mafi ƙololuwa, saboda yiwuwar samun mahaukaciyar guguwa a ranar Litinin, bayan mahaukaciyar guguwa mai ƙarfin gaske ta Belal ta auka masa.

    Mahukunta sun gargaɗi mazauna tsibirin da su zauna a gidajensu, yayin da aka dakatar da duka ayyukan kai ɗauki.

    Matsanancin yanayin ya janyo asarar rayuka a tsibirin biyu na Réunion da kuma Mauritius.

    An tsinci gawar wani mutum da bashi da matsuguni a wurin shaƙatawa da ke ƙauyen Saint-Gilles a gaɓar yammacin Réunion, gab da sauya ma'aunin gargaɗin zuwa mafi tsanani a ranar Litinin.

    Hukumomi sun ce mutumin ya ƙi yarda a ɗauke shi daga wurin.

    A ƙauyen Baie-du-Tombeau a Mauritius, ruwa ya cinye wani dattijo mai shekara 75 a ranar Lahadi.

    Guguwar ta auka wa wasu mutane biyu masu wasa a tekun La Preneuse da ke yammacin Mauritius.

    Mutum ɗaya ya samu isa gaɓar tekun, ɗayan kuma ba a san inda ya yi ba.

    • 'Yadda surukata ta ɓata cikin laka bayan mahaukaciyar guguwa'
    • Mahaukaciyar guguwa da ta shafe fiye da wata ɗaya tana ɓarna
  9. Yadda kisan ɗaya daga ƴan mata shida a hannun masu garkuwa ya fusata ƴan Najeriya

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Al'umma a Najeriya, musamman ma a shafukan sada zumunta na nuna ɓacin ransu bayan da masu garkuwa da mutane suka kashe wata budurwa bayan sace ta da ƴan'uwanta a birnin Abuja.

    Ƴan bindiga ne suka yi dirar mikiya a gidansu da ke yankin Bwari a Abuja tare da harbe ƴan sanda uku kafin daga bisani su yi garkuwa da ƴan matan da mahaifinsu.

    A cewar rahotanni, ƴan bindigar sun halaka Nabeehah - ɗaya daga cikin ƴan matan a ƙarshen mako wadda ɗaliba ce a jami'a bayan da danginta suka gaza biyan kuɗin fansa.

    Wani ɗan uwan ƴan matan ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa ƴan bindigar sun miƙa wa ƴan uwan Nabeehah gawarta.

    Ƴan bindigar dai sun yi barazanar halaka ƴan'uwan Nabeehah da ke hannunsu idan ba a biya su kuɗin fansa ba nan da ranar Laraba.

    Biyu daga cikin ƴan sanda uku da ƴan bindigar suka harba a lokacin da suka kai hari suma sun mutu kamar yadda rahotanni ke bayyanawa.

    Ƴan sanda sun ce suna yin duk mai yiwuwa domin kuɓutar da ƴan matan sai dai ba su tabbatar da mutuwar Nabeehah ba.

    Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ya ce kisan Nabeehah wata tunatarwa ce cewa ƴan bindiga na cin karensu ba babbaka a ƙasar inda kuma ya yi kira a kawo gyara a harkokin tsaron ƙasar.

    Shi ma Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyyar Labour ya ce batun garkuwa a babban birnin ƙasar manuniya ce kan rashin tsaro a sauran sassan ƙasar.

    • Abun da muka sani kan Nabeeha da ƴan'uwanta da aka sace a Abuja
    • Yadda matsalar tsaro ta addabi al’ummomin Bwari a Abuja
  10. Barka da hantsi!

    Masu bibiyar mu a wannan shafi na Kai Tsaye, assalamu alaikum. Da fatan mun wayi gari a wannan rana ta Litinin - tushen aiki, lafiya.

    Kamar yadda muka saba, za mu kawo muku labarai da rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ƙasashe maƙwabta.

    Akwai shafukanmu na sada zumunta - Fesbuk da X da Instagram inda a nan ma akwai ƙarin labaran da za ku iya karantawa har ma da bidiyo da za ku iya kalla.