Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni daga sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Nabeela Mukhtar Uba, Ahmad Tijjani Bawage, Mukhtari Adamu Bawa and Abdullahi Bello Diginza

  1. An bai wa Cabo Verde shaidar rabuwa da zazzabin cizon sauro

    ..

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ayyana Cabo Verde a matsayin ƙasar da ta rabu da zazzabin cizon sauro - wani muhimmin ci gaba ga fannin lafiya.

    A yanzu ƙasar ta shiga jerin ƙasashe 43 da yanki ɗaya da WHO ta bai wa wannan shaida ta rabuwa da cutar ta maleriya.

    Cabo Verde ce ƙasa ta uku a nahiyar Afirka da ta samu wannan shaida daga WHO baya ga Mauritius da aka tabbatar ba ta da cutar a shekarar 1973 sai Algeriya a 2019.

    Shugaban hukumar WHO, Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus ya yaba wa gwamnatin Cabo Verde saboda jajircewarta wajen kawar da cutar ta zazzaɓin cizon sauro.

    "Shaidar da WHO ta bai wa Cabo Verde na rabuwa da maleriya na nuna tasirin tsare-tsaren da suka shafi lafiyar al'umma." in ji Dr Ghebreyesus.

    Dr Dorothy Achu, jami'ar WHO a Afirka ta shaida wa BBC cewa an ɗauki matakai sosai kafin samun wannan ci gaba.

    Ta ce "muna murna ƙwarai, mun ji daɗi sosai cewa an samu sakamako mai kyau daga ƙoƙarin likitoci da jami'an kula da ƙwayoyin cuta da ƙwararru a yankin wajen ganin an kawar da maleriya daga Afirka. Wannan wani fata ne, wannan ya ƙara mana ƙwarin gwiwa cewar mai yiwuwa ne a cimma haka. Ita ce ƙasa ta farko, Cabo Verde, ƙasa ta farko cikin shekara 50 da ta gabata a yankin kudu da hamadar sahara da ta samu wannan ci gaba."

    Cutar zazzabin cizon sauro ta fi ƙamari a nahiyar Afirka da ke da kusan kashi 95 cikin 100 na masu fama da ita sai kashi 96 cikin 100 na mace-macen da ke da nasaba da cutar a 2021.

  2. An tsare tsohon ministan Kenya a Uganda kan zargin safarar zinare

    Kenya

    Asalin hoton, Uganda Revenue Authority

    Hukumomin Uganda na tsare da tsohon mataimakin ministan harkokin tsaron cikin gidan Kenya Stephen Tarus bisa zargin safarar zinare zuwa cikin ƙasar ta hanyar amfani da takardun jabu.

    Wata kotun yaƙi da cin hanci da rashawa ta Uganda ce ta kama.

    Hukumar tara kudaden shiga ta Uganda (URA) ta ce an kama Mista Tarus ne a makon da ya gabata, kuma an gurfanar da shi a gaban wata kotun yaki da cin hanci da rashawa ta ƙasar ranar Larabar da ta gabata, bisa samunsa da laifin karkatar da takardun fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.

    Takardun cinikin ba bisa ka'ida ba sun haifar da asarar kuɗaɗe ga gwamnatin Uganda, in ji URA.

    An tuhume shi da yin jabun takardu na fitar da kaya akan kilogiram 13 na zinari da darajarsu ta kai $30,000.

    Wata ƙungiya da ake zargi ta safarar mutane ce ta yi niyyar tafiya da zinaren zuwa Dubai, kamar yadda URA ta ruwaito.

    An tsare Mista Tarus a gidan yarin Luzira har zuwa ranar 18 ga watan Janairu, inda ake ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

    Sai dai har yanzu bai ce uffan ba kan zargin.

    Ɗan shekara 57 ya taɓa rike mukamin mataimakin minista a karkashin marigayi shugaba Mwai Kibaki da kuma jakadan Kenya a Australia tsakanin shekarar 2009 zuwa 2012.

    Ya kuma zama ɗan majalisa tsakanin 2003 zuwa 2007.

  3. Kotun ƙoli ta tabbatar da nasarar gwamna Sanwo-Olu na Legas

    ..

    Asalin hoton, BABAJIDE SANWO-OLU

    Kotun Ƙoli ta tabbatar da Babajide Sanwo-Olu a matsayin halastaccen gwamnan jihar Legas.

    Alƙali Garba Lawal ne ya gabatar da hukuncin inda ya kori ƙarar da Gbadebo Rhodes-Vivour na jam'iyyar Labour ya ɗaukaka saboda rashin cancanta.

    Sakamakon zaɓen gwamnan jihar ya nuna cewa Sanwo-Olu ya yi nasara ne a zaɓen da ƙuri'u 762,134.

    Jam'iyyar LP ce ta zo ta biyu inda ɗan takararta Gbadébo Rhode-Vivour ya samu ƙuri'u 312,329, sai kuma ɗan takarar jam'iyyar PDP Abdulazeez Olajide Adeniran da ya zo na uku da ƙuri'u 62,449.

  4. An tsaurara tsaro a harabar Kotun Ƙolin Najeriya

    ..

    Asalin hoton, Supreme Court

    An tsaurara matakan tsaro a dukkan hanyoyin da za su kai ga kotun ƙolin Najeriya da ke Abuja, inda ake zaman yanke hukunci kan zaɓukan gwamna da aka ɗaukaka daga wasu jihohin ƙasar.

    Jihohin su ne Kano da Legas da Filato da Bauchi da Ebonyi da Zamfara da Cross River.

    Shari'oin zaɓen gwamnan Kano da Filato na daga cikin waɗanda hankali ya fi karkata a kan su kasancewar su ne waɗanda ƙananan kotuna suka rushe zaɓen gwamnonin da ke ci.

    A cewar bayanai, jami'an tsaro sun hana ƴan jarida da lauyoyi da ƴan siyasa da ba su da shaidar shiga harabar kotun.

  5. Mai magana da yawun gwamna Zulum Isa Gusau ya rasu

    Isa Gusau

    Asalin hoton, Isa Gusau/Facebook

    Mai magana da yawun gwamnan jihar Borno, Isa Gusau, ya rasu.

    Rahotanni sun bayyana cewa Isa Gusau ya rasu ne a da yammacin ranar Alhamis a ƙasar Indiya bayan shafe lokaci yana jinya.

    Gusau ya fara aikinsa na mataimaki kan harkokin yaɗa labarai ne tun lokacin tsohon gwamnan Borno, Kashin Shettima, mataimakin shugaban Najeriya a yanzu.

    Bayan karewar wa'adin Shettima ne, gwamna Babagana Umara Zulum ya sake naɗa shi a matsayin mai magana da yawunsa a 2019, muƙami da ya riƙe har zuwa miutuwarsa.

    Jama'a da dama dai ciki har da ƴan uwa da abokai ke ta alhinin rashinsa, inda aka bayyana shi a matsayin hazikin mutum kuma mai nagarta.

  6. Hotuna: Gwamna Abba Kabir da Gwamna Bala sun isa Kotun ƙoli

    ..

    Asalin hoton, Sanusi Bature/Facebook

    Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf na Jam'iyyar NNPP ya isa harabar Kotun ƙoli da za ta yanke hukunci kan ƙarar da ya ɗaukaka don ƙalubalantar hukuncin kotun ɗaukaka ƙara da ta soke nasararsa.

    Gwamna Abba Kabir yana ƙalubalantar hukuncin ne bayan da ƙananan hotuna suka bai wa tsohon mataimakin gwamnan Kano, Nasiru Yusuf Gawuna nasara.

    Tun da farko, kotun zaɓen gwamnan Kano a watan Satumban 2023 ce ta soke ƙuri'a 165,633 wadda in ji ta, aka yi wa ɗan takarar na jam'iyyar NNPP aringizo, bayan hukumar zaɓe a watan Maris, ta ce ya samu ƙuri'a 1,019, 602.

    ..

    Asalin hoton, Sanusi Bature/Facebook

    Bayanan hoto, Gwamna Abba Kabir Yusuf tare da mataimakinsa Aminu Abdussalam Gwarzo (Hagu)

    Shi ma gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed na jamiyyar PDP ya isa kotun ƙolin bayan da ɗan takarar Jam'iyyar APC a zaben da aka yi bara, Saddique Abubakar ya shigar da ƙarar ƙalubalantar nasarar gwamnan.

    Tun da farko, kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamna ta jihar Bauchi da kotun ɗaukaka ƙara duk sun kori ƙararsa, suna cewa ba ta da tushe.

    Saddiqu Abubakar dai ya yi iƙirarin cewa takardun zaɓe masu yawa da aka yi amfani da su, ba a cike su yadda ya kamata ba. Sannan ya yi zargin cewa ba a yi biyayya ga kundin dokokin zaɓe a lokacin kaɗa ƙuri'ar zaɓen gwamna a Bauchi ba.

    ..

    Asalin hoton, Sanusi Bature/Facebook

    ...

    Asalin hoton, Sanusi Bature/Facebook

    Bayanan hoto, Gwamna Abba Kabir tare da takwaransa na jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare. Shi ma ya ɗaukaka ƙara zuwa kotun ƙoli yana neman ta tabbatar da nasararsa, wadda kotun baya ta soke, har ma ta ba da umarnin a yi sabon zaɓe cikin wasu ƙananan hukumomi.
    ..

    Asalin hoton, Sanusi Bature/Facebook

    Bayanan hoto, Gwamna Abba Kabir tare da gwamnan Plateau, Caleb Mutfwang wanda ya garzaya gaban kotun bayan kotun ɗaukaka ƙara a watan Nuwamba ta rushe zaɓensa, inda ta umarci Inec ta bai wa abokin shari'arsa shaidar cin zaɓen watan Maris.
  7. Iran da Hezbollah sun yi allah-wadai da harin ƙawancen Amurka da Birtaniya

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta yi tur da hare-haren awancen da Amurka da Burtaniya suka kai kan Yemen inda ta bayyana hakan a matsayin "take ƴancin gashin kan Yemen ƙarara da kuma take dokokin ƙasa da ƙasa.

    Ta ce babu abin da hare-haren za su haifar illa ingiza matsalar tsaro a yankin kamar yadda kakaknin ma'aikatar Nasser Kanani ya ce a wani saƙo ta shafin ma'aikatar a manhajar Telegram.

    A gefe guda kuma, ƙungiyar Hezbollah da ke Lebanon ita ma ta yi alla-wadai da jerin hare-haren.

    "Hare-haren da Amurka sun tabbatar da cewa ƙasar tana da hannu ɗari bisa ɗari a munanan labarai da kuma kashe-kashen da maƙiya ke yi a Gaza da kuma yankin", in ji ƙungiyar kamar yadda Reuters ta ruwaito.

  8. Ƴan sanda sun haramta tarukan siyasa gabanin hukuncin kotun ƙoli kan zaɓen Zamfara

    ..

    Rundunar ƴan sanda a Zamfara ta haramta taruka da gangamin siyasa gabanin hukuncin kotun ƙoli kan zaɓen gwamnan jihar.

    Kwmaishinan ƴan sanda na jihar Zamfara, Muhammad Dalijan ne ya sanar da haramcin yayin da ake dakon hukuncin da kotun ƙolin za ta yanke kan ƙarar da gwamna Dauda Lawal ya shigar gabanta inda yake neman a soke hukuncin kotun ɗaukaka ƙara da ya buƙaci a sake zaɓe a jihar.

    Kwamishinan ƴan sandan ya kuma ja kunnen magoya bayan jam'iyyar APC da na PDP da su guji furta kalaman da ka iya yamutsa hazo.

    Ya ce jami'an tsaro za su sa ido tare da hukunta duk wanda aka samu da tada hayaniya a jihar.

    A cewarsa, an baza ƴan sanda a lungu da saƙo na jihar domin tabbatar da doka da oda inda kuma ya nemi jama'ar jihar da su ci gaba da tafiyar da harkokinsu.

  9. Assalamu Alaikum!

    Jama'a barkan mu da wannan babbar rana ta Juma'a. Da fatan mun wayi gari lafiya.

    Kamar kullum, za mu kawo muku labarai da rahotannin wainar da ake toyawa a ƙasashen duniya musamman Najeriya da ƙasashe maƙwabta.

    Da fatan za ku kasance tare da mu.