Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni daga sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Ahmad Tijjani Bawage, Haruna Kakangi, Nabeela Mukhtar Uba and Abdullahi Bello Diginza

  1. CBN ya naɗa sabbin shugabannin bankunan Polaris da Union da Keystone

    CBN

    Asalin hoton, CBN/X

    Babban bankin Najeriya CBN ya naɗa sabbin shugabannin wasu bankunan kasuwanci a Najeriya.

    Wata sanarwa da CBN ɗin ya fitar a ranar Alhamis, ya ce bankunan da aka naɗa shugabannin sun haɗa da Polaris, Keystone da kuma Union.

    Sanarwar ta CBN ta ce an naɗa Lawal Mudathir Omokayode Akintola, a matsayin shugaban bankin Polaris, sai Hassan Imam, wanda ya zama sabon shugaban bankin Keystone.

    Sai kuma Yetunde Oni a matsayin shugabar bankin Union.

    Naɗa sabbin shugabannin na zuwa ne bayan rusa kwamitocin gudanarwar bankunan da CBN ya yi saboda karya dokoki da suka yi, ciki har da shiga ayyukan da suke barazana ga harkokin kuɗi.

    • CBN ya ce a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudi
    • Me ya sa ake ƙarancin takardun naira a sassan Najeriya?
    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. Mutum 15 sun mutu a sabuwar tarzoma da ta ɓarke a Papua New Guinea

    Papua New Guinea

    Asalin hoton, Getty Images

    Mutane 15 ne aka rawaito sun mutu a tarzoma da tashin hankalin da ya ɓarke a Papua New Guinea.

    Lamarin ya fara ne daga babban birnin ƙasar, Port Moresby bayan 'yan sanda sun tafi yajin aiki kan rashin albashi da ingancin aiki.

    Nan da nan tarzoma ta fara ɓarke a can, inda mutane su ka yi amfani da damar wajen fasa shagunan 'yan kasuwa da sace kayayyaki.

    Firaiminista James Marape ya faɗa wa manema labarai cewa ya bai wa mutanen da aka yi wa sata a wuraren kasuwanci da gidajensu hakuri, inda ya ce gwamnati za ta taimaka musu wajen farfaɗo da kasuwancinsu.

  3. MDD ta yi kiran dakatar da kai wa jiragen ruwa hari a tekun Maliya

    Tekun Maliya

    Asalin hoton, PA Media

    Kwamitin tsaro na MDD ya yi kiran a gaggauta kawo karshen kai wa jiragen ruwa hari a tekun Maliya da 'yan tawayen Houthi da Iran ke marawa baya ke yi a tekun Maliya.

    Houthi dai na kai hare-haren a daidai lokacin da ake nuna damuwa kar rikici ya barke ayankin gabas ta tsakiya kan yakin da ake yi a Gaza.

    Kwamitin ya yanke hukuncin mambobin kasaseh na da damar kare jiragensu da ke ratsawa tekun maliya.

    Jakadan Japan a MDD Kazuyuki Yamakazi, ya ce matakin ya aike da kakkausan sako.

    Wannan zai tabbatar da cewa kwamaitin tsaro na MDD ba zai amince da abin da Houthi ke yi a tekun Maliya ba, da bai wa mambobin ƙasashe kwarin gwiwa.

  4. Buɗewa

    Masu bibiyar mu barkan mu da safiyar Alhamis.

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa.

    Ku kasance da mu don samun abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da kuma sauran sassan duniya.

    Ahmad Tijjani Bawage ke tare da ku a wannan safiya!