ISIS ta ɗau alhakin harin da aka kai Kabul
Ƙungiyar SISI mai ikirarin jihadi ta ɗauki alhakin kai harin da aka kai Kabul a jiya Talata, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum uku. Hari na biyu da aka kai birnin a mako guda.
Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta kafar Telegram, wanda ta ce ta nufi ma'aikatar gidan yarin Pol Charkhi" wanda ya yi sanadin mutuwar mutum 10.
Kakakin Taliban a Kabul Khaled Zadran ya sanar da hakan ne a jiya, inda ya ce mutum uku ne suka mutu wasu huɗu na daban suka jikkata, a harin da suka kai dalilin ajiye wani abun fashewa a cikin mota. Ya ce duka mutanen da abun ya rutsa da su "fararen hula ne".
Kwanaki hudu da uka gabata, mutum biyar sun mutu, 15 kuma suka jikkata a yankin Shi'a da Hazara da ke Kabul wanda shi ma ISIS suka dauki alhaki.





