Amurka za ta kai Koriya ta Arewa ƙara a kan tallafa wa Rasha da makamai

Fadar White House ta ce Koriya ta Arewa na ƙara yawan makamai masu linzami da take taimaka wa ƙasar Rasha domin ci gaba da kai wa Ukraine hare-hare.
Kakakin ma'aikatar tsaron kasar, John Kirby, ya ce dakarun Rasha suna amfani da makaman wajen kai hare-hare cikin Ukraine.
Ya ce wannan babban abun damuwa ne a taimakon da Korea ta Arewa ke ba wa Rasha, kuma Amurka za ta kai korafinta ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.
Harwayau, Mista Kirby ya kuma yi ikirarin cewa Rashar na neman gudummawar makamai daga Iran.
Ko a watan Disambar da ya gabata sai da Rashar ta kai wa kasar Ukraine wani hari irinsa mafi muni tun fara yakin, inda aka samu rashe-rashe da jikkata da kuma lalata gine-gine.




