Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni daga sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Mukhtar Adamu Bawa and Usman Minjibir

  1. Blinken zai ziyarci Gabas ta Tsakiya karo na hudu tun fara yakin Isra'ila

    ..

    Asalin hoton, Reuters

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken zai kai ziyara Gabas ta Tsakiya karo na huɗu, tun bayan da yaƙi ya ɓarke tsakanin Hamas da Isra'ila cikin watan Oktoba.

    Wani jami'in Amurka ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP da Reuters cewa ziyarar za ta haɗa da zuwa Isra'ila daidai lokacin da ake bayyana damuwa game da tasirin yaƙin ga yankin.

    Jami'in ya ce a daren yau, Alhamis ne Blinken zai yi bulaguron inda zai ziyarci wasu ƙasashen har da Isra'ila.

    Sai dai babu ƙarin haske game da yadda jadawalin tafiyar tasa zai kasance.

    Lamarin na zuwa ne bayan kashe ɗaya daga cikin jagororin kungiyar Hamas, Saleh al-Arouri, a Beirut, abin da ya sa ƙungiyar Hezbollah ta ce "za ta mayar da martani".

    Isra'ila ba ta tabbatar ko musanta hannunta a harin ba, sai dai wani jami'i ya ce hari ne kan shugabancin Hamas.

    • Ya kamata a daina ci da gumin 'yan Afirka - Blinken
  2. An kashe mambobin Hezbollah huɗu a wani hari ta sama

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Ƙungiyar Hezbollah da ke samun goyon bayan Iran ta ce an kashe huɗu daga cikin mambobinta a abin da kafofin yaɗa labaran ƙasar suka ce hari ne da Isra'ila ta kai ta sama kan ƙauyen Naqoura.

    Gidan Talabijin na Al Manar ya ce mutanen huɗu sun yi shahada kuma a cewar wata sanarwa da aka fitar a daren jiya, Laraba, daga cikin waɗanda suka mutu akwai jami'in ƙungiyar Hezbollah.

    Kamfanin dillancin labarai na Lebanon ya ruwaito jirgin na Isra'ila ya jefa bom kan wani gini mai hawa uku lamarin da ya ruguza ginin baƙi ɗaya.

    Ya kuma ba da rahoton jikkatar wasu farar hula gudana tara sakamakon harin.

    Jaridar The Times ta Isra'ila ta ce adadin mambobin Hezbollah da aka kashe tun soma yaƙin a Oktoba sun zarce 150.

    Isra'ila da Hezbollah sun shafe watanni suna kai wa junansu hare-hare.

    Zuwa yanzu, Isra'ila ba ta ce komai ba a kan harin.

    A daren jiya, rundunar sojin Isra'ila ta wallafa wani bidiyo a shafin intanet wanda ta ce ya nuna tana kai hare-hare kan cibiyoyin Hezbollah a yankunan Lebanon.

    Hoton bidiyon ya nuna yadda aka kai hari kan gine-gine da dama daga bisani kuma aka ga fashewar abubuwa da hayaƙi na tashi.

    • Abin da ya kamata ku sani kan jagoran kungiyar Hezbollah
    • Mun samu rokokin zamani duk da kokarin Isra'ila na hana mu - Hezbollah
  3. An kama matashin da ake zargi ya yi wa ƴar'uwarsa ciki amma ta mutu wajen zubarwa

    ..

    Asalin hoton, Kano State Police Command

    Rundunar 'yan sandan Najeriya reshen jihar Kano ta ce ta kama wani likitan bogi mai suna Chidera Ugwu bisa zarginsa da yi wa wata mai juna biyu allura lamarin da ya yi sanadin mutuwarta.

    Wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce ta kama likitan bogin ne bayan samun wani rahoto kan wani matashi Ukasha Muhammad mai shekara 19 a ƙauyen Langel da ke ƙaramar hukumar Tofa, wanda ake zargi ya yi wa ƴar'uwarsa ciki, amma ya haɗa baki da Chidera domin yi wa matashiyar allura da nufin zub da cikin.

    Sai dai a cewar sanarwar, an samu akasi inda allurar da Chidera ya yi wa matashiyar ta yi sanadin mutuwarta.

    A cewar rundunar, matasan biyu sun amsa laifin da ake zarginsu da aikatawa. Ko da yake, BBC a karan kanta ba ta iya tabbatar da hakan ba.

    Sanarwar ta ce ana zargin Chidera Ugwu ya saba yi wa mata masu ciki allurar da take haddasa mutuwarsu, kamar yadda binciken da rundunar ƴan sandan ta ce ta yi ya nuna.

    Rundunar ta kuma ce ta kama wani matashi Yusuf Haruna daga ƙaramar hukumar Dala wanda ake zargi da kashe wani fitaccen limami ta hanyar daɓa masa wuƙa.

    Matashin ya daɓa wa limamin mai suna Mallam Sani Mohammed Shuaibu wuƙar ne a bayansa a lokacin da yake alwala.

    A cewar sanarwar, an garzaya da limamin asibitin ƙwararru na Murtala Muhammad inda kuma likita ya tabbatar ya mutu saboda ciwon da ya ji.

    Sanarwar ta bayyana cewa matashin ya yi aika-aikar ne saboda yadda limamin ya sha gargaɗinsa da ƴan tawagarsa kan su daina busa tabar wiwi a harabar masallaci.

    Runudnar ta ce za ta gudanar da bincike kan laifukan biyu domin tabbatar da adalci ga waɗanda suka rasa rayukansu.

    • 'Hana 'yan mata masu ciki zuwa makaranta a Saliyo ba daidai ba ne'
    • Za a daure likitan da ya zub da ciki tsawon shekara 90
  4. Sadiya Farouq ta ce rashin lafiya ne ya hanata zuwa – Majiyar EFCC

    ..

    Asalin hoton, @SADIYA_FAROUQ/X

    Wata majiya daga hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arzikin Najeriya zagon ƙasa ta shaida wa BBC dalilin da ya sa tsohuwar ministar jin ƙai, Sadiya Umar Farouq ba ta amsa gayyatar hukumar ba.

    A cewar majiyar, tsohuwar ministar, wadda ake zargin ta da hannu a badaƙalar halasta kuɗin haram naira biliyan 37.1 ta nemi EFCC ta ƙara mata lokaci saboda dalilai na rashin lafiya.

    Tun farko, kafofin yaɗa labaran Najeriya sun ruwaito cewa tsohuwar ministar ba ta bayyana a hedikwatar hukumar ta EFCC ba.

    A farkon makon jiya ne, Sadiya Umar Farouq ta fitar da wata sanarwa, wadda a ciki ta musanta hannu a badaƙalar da ake zargi. Ta ma yi iƙirarin cewa kwata-kwata ma ba ta san ɗan kwangilar da rahotanni ke cewa hukumar EFCC ta kama a binciken da take yi dangane da batun ba.

    Wata majiya daga EFCC a ranar Laraba ta tabbatarwa da BBC cewa hukumar na sa ran isar tsohuwar ministar ta zamanin Shugaba Muhammadu Buhari, zuwa ofishinsu da ke Abuja.

    Sai dai jaridar Punch ta ruwaito cewa jami'an EFCC sun shafe tsawon sa'o'i suna dakon isar Sadiya Farouq, amma har lokaci ya ƙure ba su ga tsohuwar ministar ba, kuma ba tare da samun wani bayani daga gare ta a kan dalilinta na gaza bayyana a hukumar ba.

    EFCC dai ta gayyace ta ne tun a makon jiya domin ta yi ƙarin haske game da zargin halasta kuɗin haram a ƙarƙashin shugabancinta.

    A saƙon da ta wallafa a shafinta na X, tsohuwar ministar ta ce "Akwai rahotanni da dama da ke alaƙanta ni da wani bincike na hukumar EFCC game da ayyukan wani james Okwete, kwata-kwata ma ni ban san shi ba.".

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    • Mun sauke nauyin da aka ɗora mana - Sadiya Umar Farouk
    • Sadiya Umar Farouq ta ce sun kashe fiye da N500m don ciyar da ɗalibai lokacin kulle
  5. Donald Trump na ƙalubalantar cire sunansa daga takara

    Trump
    Bayanan hoto, Jihar Colarado ta cire sunan Trump daga takardar kuri'a

    Tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya bukaci kotun kolin kasar ta yi watsi da matakin da jihar Colorado ta dauka na cire sunansa daga takardar kuri'a, a jihar, a zaben watan Nuwamba.

    Mista Trump wanda ya fi farin jini cikin masu neman takara a jam'iyyar Republican, inda ya ce aikin Majalisar wakilai ne ayyana wanda zai iya rike ofis, ba jihohi ba.

    A watan da ya gabata ne babbar kotun jihar Colorado ta ce ta cire Mista Trump daga masu takara saboda rawar da ya taka a harin Majalisar Dokokin kasa ta Capitol, a Washington, shekaru uku da suka gabata.

    • Kotu ta haramta wa Trump tsayawa takara
  6. Kasashen duniya sun gargadi mayakan Houthi, Amurka da Isra'ila sun gargadi 'yan Houthi

    Houthi
    Bayanan hoto, Mayakan Houthi na samun goyon bayan Iran

    Sanarwar hadin gwiwa da wasu kasashe goma sha biyu suka fitar ciki har da Amurka ta gargadi 'yan tawayen Houthi a Yemen kan ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa na kasuwanci a tekun Maliya.

    Sanarwar ta ce mayakan su kuka da kansu, idan suka ci gaba da yin barazana ga rayuka da 'yancin zirga-zirga.

    Masharhanta na ganin da alama wannan gargadi mafarin daukar matakin soji ne a kan Yemen.

    Yawancin manyan kamfanonin sufurin jiragen ruwa na duniya a yanzu na kauucewa tekun Maliya, inda suke bi ta kudancin Afirka, abun da ke daukar lokaci mai tsawo.

    • Me ya sa 'yan Houthi ke kai hari kan jiragen ruwa?
    • Mayaƙan Houthi sun harbawa Saudiyya makami mai linzami
  7. Iran ta shiga makoki bayan harin bam da ya halaka kusan mutum 100

    ..

    Asalin hoton, ANADOLU

    Iran ta shiga makokin yini guda domin jimamin mutanen da suka mutu sakamakon wani bom da ya tashi ana tsaka da taron tunawa da babban kwamandan sojin ƙasar Qasem Soleimani.

    Kusan mutum 100 ne suka mutu sakamakon bama baman da suka tashi kuma Iran ta zargi Isra'ila da Amurka da kai harin.

    Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka ya yi watsi da zargin da Iran ta yi inda ya ce abin dariya ne.

    Shugaban Iran, Ibrahim Raisi ya gargaɗi Iran da cewa za ta girbi abin da ta shuka.

    Bama baman sun tashi kusa da maƙabarta inda dubban mutane suka taru domin tunawa da babban kwamandan sojin ƙasar da wani jirgin Amurka maras matuƙi ya kashe shekaru huɗu da suka gabata.

    • Wane ne jagoran Hamas da aka kashe a Beirut?
    • Isra'ila ta ɗau alwashin ci gaba da kai farmakin soji a Gaza har sai ta cimma burinta
  8. Barka da warhaka!

    Masu bibiyarmu a wannan kafa, barkan mu da safiya. Da fatan kun tashi cikin ƙoshin lafiya.

    A yau ma, wannan shafi na Kai Tsaye zai wallafa muku labarai da rahotanni na wainar da ake toyawa a ƙasashen duniya.

    Sai ku ci gaba da kasancewa tare da mu, kuna kuma iya garzayawa shafukanmu na sada zumunta domin karanta wasu ƙarin labaran da ma kallon bidiyo.