An yi jana'izar limamin masallacin Juma'a da aka harbe a jihar Filato

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni daga sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Habiba Adamu and Mukhtar Adamu Bawa

  1. Morocco ta ƙwace tan 1.4 na hodar iblis da aka boye cikin ayaba

    ..

    Asalin hoton, Morocco General Directorate for National Security (DGSN)/X

    Ƴan sanda a Morocco sun ƙwace tan 1.488 na hodar iblis a wani samamen haɗin gwiwa da jami'an tsaron Spaniya.

    An gano hodar iblis din ne ɓoye cikin kwalayen ayaba da aka maƙara su cikin kwantenar kaya ta jirgin ruwa daya taho daga kudancin Amurka zuwa Turkiyya.

    An yi kamen ne a ranar Talata a tashar jirgin ruwa ta Tanger Med a arewacin Morocco.

    Mahukuntan Moroccon sun ce suna zargin an shigo da hodar iblis ɗin ne a wani yunƙuri na safarar miyagun kwayoyin zuwa ƙasashen duniya amma har yanzu suna gudanar da bincike.

    Lamarin ya faru ne kwana ɗaya bayan mahukunta sun ƙwace hodar iblis mai nauyin kilo 363 daga wata babbar mota da ke ƙoƙarin shiga Morocco ta iyakar ƙasar da Mauritania.

    An gano cewa ƙasar da ke arewacin Afrika ita ce babbar hanyar da ake amfani da ita wajen safarar miyagun ƙwayoyi daga kudancin Amurka zuwa Turai.

    • 'Kowane dare sai na yi mugayen mafarkai kan girgizar-ƙasa'
    • Malamar da girgizar ƙasa ta halaka dukkanin ɗalibanta a Moroko
  2. Wane ne jagoran Hamas da aka kashe a Beirut?

  3. Najeriya ta rufe jami'o'in ƙasashen waje 18 bayan rahoton 'digiri ɗan Kwatano'

    ..

    Asalin hoton, OTHER

    Bayanan hoto, Hukumar NUC, mai kula da jami'oin Najeriya

    Gwamnatin Najeriya ta haramtawa wasu jami'oin ƙasashen waje 18 tafiyar da harkokinsu a ƙasar inda ta bayyana su da masana'antun haɗa digiri.

    Gwamnatin ta kuma gargaɗi ƴan Najeriya su guji shiga jami'oin.

    Matakin ya shafi jami'oi biyar daga Amurka sai guda shida daga Birtaniya, uku kuma daga Ghana.

    Da take sanar da matakin dakatarwar cikin wata sanarwa, hukumar kula da jami'oin Najeriya, NUC ta yi bayani cewa jami'oin 18 ba su da sahhalewar gwamnati don tafiyar da harkokinsu a don haka ta rufe su.

    Ta ce "Hukumar NUC na sanar da jama'a musamman iyaye da ɗalibai cewa waɗannan jami'oin ba su da lasisin gwamnatin tarayya don haka an rufe su saboda take dokar ilimi ta Najeriya ta 2004.

    Daga cikin jami'oin da wannan matakin ya shafa akwai jami'ar Applied Sciences & Management da ke Jamhuriyar Benin da jami'ar Volta University College da ke Ghana sai International University da ke Missouri a Amurka da sauran cibiyoyinta da ke Kano da Legas, akwai kuma jami'ar Collumbus da ke Birtaniya.

    A jiya Talata ne ma'aikatar ilimi ta ce ta dakatar da tantance shaidar digiri daga jami'oin Benin da Togo, a wani yunƙuri na tsaftace ɓangaren ilimin, har zuwa lokacin da za ta kammala bincike a kan ingancin makarantun.

    Matakin dai ya zo ne bayan wani bincike da jaridar Daily Nigerian ta gudanar kan yadda ma'aikacinta ya samu shaidar kammala digiri daga wata jami'a a Cotonou cikin ƙasa da wata biyu.

    • Binciken da ya janyo dakatar da 'digiri ɗan Kwatano' a Najeriya
  4. 'Yan fashin daji sun sako shugaban ƙaramar hukumar Akwanga

    ..

    Asalin hoton, Safiyanu Isa-Andaha/Facebook

    Rundunar 'yan sandan jihar Nasarawa ta tabbatar da sakin shigaban karamar hukumar Akwanga wanda aka sace tare da wasu mutane uku.

    Kakakin rundunar, Ramhan Nansel ya bayyana wa BBC cewa jami'an tsaro sun kubutar da Safiyanu Isah Andaha.

    A daren ranar Laraba ne 'yan fashin dajin suka saki shugaban karamar hukumar da sauran mutane ukun da suka sace, ko da ya ke wasu rahotanni na cewa sai da aka biya kudin fansa.

    Sai dai jami'in'yan sandan ya musanta haka.

    Ya kuma kara da cewa an kai mutanen hudun babban asibitin gwamnatin tarayya da ke birnin Keffi domin duba lafiyarsu.

    A daren ranar Talata ne wasu da ake zargin 'yan fashin daji ne suka farwa motocin da ke dauke da shugaban karamar hukumar, Safiyanu Isah Andaha, kuma suka yi awon gaba shi.

    Matsalar sace mutane domin karbar kudin fansa ta zamo tsumagiyar kan hanya fyale yaro fyade babba, inda ta shafi masu manyan mukamai, masu hannu da shuni, shugabannin al'umma, sarakunan gargajiya da malaman addini da kuma talakawan kasar.

    • Yadda na rasa 'yan uwana huɗu a harin Nasarawa
    • Shin me ya sa hare-haren 'yan fashin daji ke dawowa a Najeriya?
    • Satar mutane a Najeriya: Yaya munin lamarin yake?
  5. 'Rasha ta harba makamai masu linzami fiye da 500 kan Ukraine'

    ..

    Asalin hoton, BBC/TOBY LUCKHURST

    An ji ƙarar fashewar abubuwa masu ƙarfi a Sevas-topol birni mafi girma a Crimea da Rasha ta mamaye.

    Gwamnan yankin Mikhail Razvo-zhayev ya ce an kakkaɓo wani makami mai linzami da Ukraine ta harba a kan ruwa.

    Ya ce ba a samu asarar rai ba.

    An kuma ji ƙarar fashewar wasu abubuwa a birnin Belgorod na ƙasar Rasha, inda jami’ai suka ce mutum ɗaya ya mutu.

    Yaƙin da ake gwabzawa tsakanin ɓangarorin biyu ya ƙara ƙamari tun a ƙarshen watan jiya.

    A cewar shugaba Volodymyr Zelensky, Rasha ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi sama da ɗari biyar a kan Ukraine cikin kwanaki biyar da suka gabata.

  6. Kashe ɗaya daga jagororin ƙungiyarmu ba zai girgiza aniyarmu ba – Hamas

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Shugaban Hamas Ismail Haniyeh, ya ce kisan mataimakin na sa ba zai kawo naƙasu ga aniyar ƙungiyar na ci gaba da yin turjiya don ƴantar da Falasɗinawa daga gashin ƙumar da Isra'ila ke yi musu ba.

    Wata mai magana da yawun sakataren Majalisar Dinkin Duniya Florencia Soto Nino, ta ce harin abin tayar da hankali ne.

    Ta ce ci gaba da wannan yaƙi na tattare da haɗarin ɗaukar wani mataki da ka iya zama gagarumin kuskure.

    Ƙungiyar Hezbullah ta Lebanon ta ce Isra'ila za ta ɗanɗana kuɗarta sakamakon harin a wurin da ke ƙarƙashin ikonta.

    Bayanai na cewa Isra'ila ta shiga cikin shirin ko ta kwana a iyakar arewa, yayin da take dakon irin martanin da kungiyar za ta mayar.

  7. Lebanon na zargin Isra'ila da iza wutar rikici a sassan Gabas ta Tsakiya

    Ana ta kiraye-kirayen a kai zuciya nesa, bayan kashe wani jigo na ƙungiyar Hamas a Beirut da Isra'ila ta yi.

    Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya yi gargaɗi game da duk wani shiri na kai hari Lebanon, yayin waya da Benny Gantz, mamba a majalisar ministocin yaƙin Isra'ila.

    Gwamnatin Lebanon ta zargi Isra'ila da neman ƙyasta wutar yaki a gabas ta tsakiya, bayan wani harin bam da ta kai birnin Beirut da ya kashe mataimakin shugaban ƙungiyar Hamas Saleh Al'arori.

    Wakiliyar BBC ta ce Firaministan Lebanon Najib Mikati, ya ce Isra'ila na so ne ta janyo Lebanon cikin yaƙin, wanda hakan ihu bayan hari ne, da zummar karkatar da hankalin duniya daga kan kayin da ta sha a ranar 7 ga watan Oktoba.

    Saleh al-Arouri, ya rasa ransa da wasu manyan kwamandojin Hamas yayin harin na jirgi marar matuki.

    • Wane ne jagoran Hamas da aka kashe a Beirut?
    • Mene ne tukwicin zaman lafiya a yaƙin Isra'ila da Hamas?
  8. Barka da hantsi!

    Masu bibiyar mu a wannan shafi na Kai Tsaye, barka da warhaka. Da fatan kun wayi gari lafiya.

    Kamar kullum, za mu riƙa wallafa muku labarai da rahotanni na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya.

    Sai ku ci gaba da kasancewa tare da mu domin sanin abubuwan da duniya ke ciki. Akwai wasu ƙarin labaran a shafukanmu na sada zumunta - Fesbuk da X da kuma Instagram.