Kotun Ƙoli za ta saurari ƙarar zaɓen gwamnan Kano ranar Alhamis

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Haruna Kakangi and Umar Mikail

  1. An shiga rana ta ƙarshe ta yaƙin neman zaɓe a Congo

    ..

    Asalin hoton, Reuters

    A yau Litinin ne za a kammala yaƙin neman zaɓe a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo, kwana biyu kafin masu zaɓe su jefa ƙuri'a.

    Rashin tsaro da batun lafiya da ilili na cikin manyan batutuwan da suka mamaye yaƙin neman zaɓe yayin da ƙasar ke shirin shiga zaɓe mai zafi.

    Babu masaniya kan ko zaɓukan za su gudana a gabashi inda gomman ƴan bindiga ke cin karensu ba babbaka.

    Gwamnati na amfani da jiragen sama na sojojin Congo da na Masar da dakarun wanzar da zaman lafiya na Monusco domin jigilar ragowar kayayyakin zaɓe, kamar yadda kakakin gwamnati Patrick Muyaya ya bayyana ranar Lahadi.

    An tantance fiye da yan takara 12 har da Shugaba mai ci Felix Tshisekedi da Denis Mukwege mai lambar yabo ta Nobel da kuma fitaccen jagoran ƴan hamayya Moïse Katumbi a matsayin waɗanda za su fafata a zaɓen.

    Ƙungiyar Human Rights Watch ta bayyana damuwa game da tashin hankali gabanin zaɓen.

    Ƴan bindiga sun kashe ƴan takara biyu na kujerar majalisar dokoki yayin da suke neman ƙuri'u.

  2. Yawan Falasɗinawa da suka mutu a Jabalia ya ƙaru zuwa 110

    Jami'an Hamas sun ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon hare-haren da Isra'ila ta kai Jabalia da ke arewacin Gaza ya ƙaru zuwa 110.

    BBC tana ƙoƙarin tattara bayanai sai dai kafin nan, ga abubuwan da muka sani kawo yanzu:

    • Hare-hare sun shafi wani rukunin gidaje ranar Lahadi, inda mutane da dama suka mutu, sai wasu 50 da ɓuraguzan gini suka rufe, kamar yadda jami'an Hamas suka ce.
    • Rundunar sojin Isra'ila ba ta fito kai tsaye ta yi magana kan abin da ya faru ba amma ta ce tana samame a yankin inda take kai hari kan wuraren ƴan ta'adda.
    • Wani ɗan jarida a yankin ya ce farar hula suna kuɓutar da waɗanda ƙasa ta rufe.
    ..

    Asalin hoton, Reuters

  3. Suka da ƙorafi a jawabin Tchiani yayin da Nijar ta cika shekara 65 da zama jamhuriya

    Janar Abdourahamane Tchiani

    Asalin hoton, Gwamnatin Jamhuriyar Nijar

    Bayanan hoto, Janar Abdourahamane Tchiani

    A yau Litinin ne ƙasar Nijar ke cika shekara 65 da zama jamhuriya sai dai lamarin na zuwa ne daidai lokacin da ƙasar ke cikin wani yanayi sakamakon takunkuman da aka ƙaƙaba mata bayan juyin mulkin da sojoji suka yi.

    Shugaban mulkin sojan kasar Janar Abdourahamane Tchiani a jawabin da ya yi wa ƴan ƙasar ya taɓo batutuwa da dama da suka shafi damina da tsaro da cin hanci da rashawa da siyasa da kuma rashin shugabanci na gari.

    Janar Tchiani ya ce "ta dalilin nasarorin da dakarun ƙasar ke samu a fage daban-daban, kwanciyar hankali ta fara dawowa inda ake samun raguwar hali na rashin tsaro a ƙasar,"

    Ya ce an samu komawar ƴan gudun hijira zuwa garuruwansu na asali, an kuma buɗe makarantu kusan 200 bayan shafe sama da shekara biyu a rufe saboda matsalar rashin tsaro a Tillaberi.

    A cewarsa an samu ci gaba ta ɓangaren samar da tsaro ga ayarin da ke samar da abinci da magunguna da kuma farfaɗowar ayyukan yau da kullum ga al'ummomi a wasu jihohin ƙasar.

    Ya kuma jinjina wa jami'an tsaron ƙasar da suka bayar da gudumawa wajen nasarorin da aka samu ta dalilin jajircewarsu.

    Takunkuman Ecowas

    Game da takun-saƙa tsakanin sojojin Nijar da ƙungiyar Ecowas kuwa, Janar Tchiani ya bayyana matakin da aka ɗauka a kan ƙasar da "rashin hankali da rashin imani da ta'addanci."

    Shugaban ya kuma yaba wa gwamnatocin Guinea da Chadi da Algeria da Equitorial Guinea da Morocco da Togo da sauran ƙasashen ƙawance da suka ba su goyon baya a lokutan da ya kira "masu wahala".

    Janar Tchiani ya ayyana kansa a matsayin Shugaban Kungiyar Ceton jamhuriyar Nijar ne bayan kwace iko a ranar 26 ga watan Yuli.

    Har yanzu sojojin da suka kifar da zaɓaɓɓiyar gwamnatin na Nijar na ci gaba da tsare Mohammed Bazoum da wasu daga cikin iyalansa.

    Duk wani yunƙuri na sulhuntawa tsakanin sojoji masu juyin mulkin da ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen Afirka ta Ecowas/Cedeao ya ci tura.

    An ƙaƙaba takunkumai a kan ƙasar, lamarin da ya haifar da taɓarɓarewar al'amura da wahalhalu ga al'ummar ƙasar.

    • Sojoji sun yi juyin mulki a Nijar
    • Wa'adin Ecowas ga Nijar ya tsunduma arewacin Najeriya cikin fargaba
  4. Sojoji sun ƙwace ragamar tabbatar da tsaro a Fadar shugaban ƙasar Somalia

    .

    Asalin hoton, AFP

    Sojojin Somalia sun karɓi aikin samar da tsaro a Fadar shugaban ƙasar da ginin majalisar dokoki da ke Mogadishu daga hannun tawagar wanzar da zaman lafiya ta tarayyar Afirka bayan shekara 16.

    Shugaba Hassan Sheikh Mohamud ya yaba wa sojojin ƙasar dangane da matakin inda ya ce hakan ya nuna farfaɗowar ikon sojojin ƙasar, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na ƙasar, Sonna ya ruwaito.

    Matakin ya zo ne yayin da sojojin Somalia suka soma ɗaukar nauyin tsaron ƙasar yayin da tawagar wanzar da zaman lafiya ta AU da ta daɗe tana yaƙar ƙungiyar al-Shabab da kare manyan gine-ginen gwamnati tun 2007, suka fara janyewa.

    Aƙalla jami'an wanzar da zaman lafiya na AU 17,000 ake sa ran za su fice daga ƙasar da ke kusurwar Afirka zuwa karshen shekara mai zuwa.

  5. An kashe Falasɗinawa 90 a hare-haren Isra'ila – Hamas

    .

    Mahukuntan Hamas sun ce wasu hare hare ta sama da Isra'ila ta kai sun yi sanadin mutuwar Falasdinawa 90 a sansanin ƴan gudun hijira na Jabalia.

    Ana ganin cewa mutane da dama sun mutu a yayin wani hari ta sama da aka kai kan wasu rukunin gidaje.

    Wakiliyar BBC ta ce wasu bidiyo da aka sanya a shafukan sada zumunta sun nuna yadda mazauna wajen ke amfani da hannayensu suna duba waɗanda suka maƙale a cikin ɓaraguzan gini.

    An kuma ƙaddamar da wasu hare hare ta saman a tsakiya da kuma kudancin Gaza inda mafi yawancin mutanen wajen da suka kai fiye da miliyan biyu ke neman mafaka.

    Babu wani martani daga Isra'ila, wadda ta haƙiƙance cewa tana kai hare harenta ne kan ƴan ta'adda.

    Ana dai ta kiraye kiraye a kan a tsagaita wuta a yaƙin kwata kwata.

  6. NCDC ta tabbatar da ɓarkewar cutar zazzabin Dengue a Sokoto

    ..

    Asalin hoton, GETTY IMAGES

    Hukumar kula da cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya, NCDC ta tabbatar da ɓarkewar cutar zazzabin Dengue a jihar Sokoto da ke arewacin Najeriya.

    Babban Daraktan hukumar ta NCDC, Dakta Ifedayo Adetifa wanda ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka fitar a Abuja, ya ce mutum 71 ake zargin sun kamu da cutar, an tabbatar da mutum 13 sun kamu sai dai babu rahoron asarar rai daga ƙananan hukumomin jihar uku da aka samu ɓullar cutar.

    Adetifa ya bayyana cewa galibin mutanen da ake zargin sun kamu da cutar ƴan shekara tsakanin 21 da kuma 40 ne inda ya ce an gano hakan cikin watan Nuwambar 2023.

    Babban daraktan hukumar ya ce ɓarkewar cutar a yanzu yana mataki na matsakaici la'akari da binciken da aka yi game da haɗarin cutar. Ya kuma ce akwai isassun kayan aiki da kuma ma'aikatan lafiyar da za su duƙufa ko da an samu ɓarkewar cutar a sauran jihohin ƙasar.

    Zazzabin Dengue cuta ce da sauro ke yaɗa ta a yankuna masu zafi da wuraren da ke maƙwabtaka da su.

    Alamominta sun hada da zazzabi da ciwon kai da tashin zuciya da amai da ciwon gaɓɓai, da fitowar ƙurji. A wasu lokuta kuma, tana iya janyo mutuwa.

    Ɓarkewar dengue a Najeriya wani ɓangare ne na ɓullar cutar a watannin baya-bayan nan a wasu ƙasashen Afirka kamar Senegal da Burkina Faso da Cabo Verde da Chadi da Ethiopia da Mali da Togo.

    A cewar wata ƙididdiga daga hukumar kare cututtuka masu yaɗuwa ta Afirka, Burkina Faso ce ƙasar da cutar ta fi ƙamari inda aka samu mutum fiye da 600.

    A watan Oktoba kuma, hukumar lafiya ta duniya, WHO ta yi gargaɗin cutar na iya bulla a kudancin Amurka da kudancin Turai da wasu sassan Afirka.

    Adetifa ya shawarci ƴan Najeriya musamman mazauna jihar Sokoto da su yi riƙo da dukkan matakan kariya kamar sanya kayan da za su rufe jikinsu domin kare kansu daga cizon sauro sannan su kwanta a gidan sauro mai magani.

    Sannan a cewarsa, ya kamata mutane su riƙa amfani da maganin sauro a wuraren da suke kwana tare da tabbatar da tsaftar muhallansu domin kare bai wa sauro mafaka.

    • Hukumar Lafiya ta sa noma a jerin cutukan da aka yi watsi da su
    • Cikakken bayani kan cutar Noma
  7. Barka da Safiya!

    Masu bibiyarmu a wannan shafi na Kai Tsaye muna muku barka da safiya. Da fatan mun wayi gari lafiya.

    A wannan kafa, muna wallafa muku rahotanni da kuma labarai kan abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

    Nabeela Mukhtar Uba ce za ta kasance tare da ku kafin miƙa ragama ga abokan aiki.

    Kuna iya garzayawa shafukanmu na sada zumunta domin kallon bidiyo da sauran labarai.