Blinken ya gana da Mahmoud Abbas a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan

Wannan shafi ne da ke kawo mu ku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza and Umar Mikail

  1. Girgizar ƙasa ta ɗaiɗaita dubban mutane a Nepal

    Sama da kwana guda kenan da girgizar kasa ta fadawa yammacin yankin Nepal, dubban wadanda abin ya shafa na ci gaba da zama a sararin Allah alhalin ana fama da muku-mukun sanyi.

    Girgizar ƙasar ta faro a daren juma'a, kuma ta fi muni a gundumar Jajakot, da yammacin Rukum.

    Sama da mutum 150 ne suka mutu wasu sama da 300 suka jikkata, amma an fara sallamar masu ƙaramin rauni daga asibiti.

    Jami'ai sun ce ana ci gaba da aikin ceto, sai dai yankin mai cunkson jama'a ne, yayin da dubban gidajen ƙasa suka baje a wurin.

  2. Ƙasashen Larabawa sun buƙaci Amurka ta sa baki don tsagaita wuta a Gaza

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministocin harkokin wajen ƙasasashen Larabawa da ke taro a Jordan, sun shaida wa sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken cewa akwai buƙatar gaggauta tsagaita wuta a Gaza.

    Takwaransa na Jordan, Ayman Safadi, ya ce Isra'ila na aikata laifukan yaƙi inda take ƙoƙarin dulmuya Gaza cikin tekun ƙiyayya, da za a ɗauki gwamman shekaru ba a manta da shi ba.

    Sai dai Mista Blinken ya jaddada musu cea Amurka na son ganin an tsagaita wutar.

    Ya ƙara da cea Amurka amince da batun tsagaita wuta da kare farar hula da shigar da agaji, da fitar da marasa lafiya.

    Mista Blinke ya ce ya yi magana da shugabannin Isra'ila kan hakan, sai dai ya ce burinsu shi ne kawar da Hamas.

  3. Barkanmu da safiya

    Masu bin mu a wanna shafi muna muku maraba da shigowa shafin kai-tsaye na BBC Hausa.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci, domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Sai ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.