'An kashe mutum 4 a rikicin da ya ɓarke a Gabar Yamma da Kogin Jordan'

Dangane da halin da ake ciki a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da ke fuskantar mamaya, rahotanni na nuni da cewa aƙalla mutane hudu sun mutu sakamakon arangamar da aka yi tsakanin Falasɗinawa da sojojin Isra'ila a Jenin.
Kamfanin dillancin labaran Wafa na ƙasar Falasɗinawa ya bayar da rahoton cewa, motocin sojin Isra'ila sun kai wani samame a garin Jenin, lamarin da ya yi sanadin lalata katangar da ke wajen asibitin Ibn Sina.
An kuma ce an harba makamai masu linzami a cikin wani gida da kuma sansanin ƴan gudun hijira na Jenin.
A martanin da kakakin sojin Isra'ila Daniel Hagari ya mayar, ya tabbatar da harin da aka kai ta sama a Jenin, inda ya ce sun kai hari tare da kawar da wasu mutane dauke da makamai.
- Isra'ila ta rushe gidajen Falasɗinawa a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan
- Mamayar Isra'ila: Abin da kuke buƙatar sani kan mamayar Isra'ila a Gabar Yamma da Kogin Jordan







