An kashe ƙarin ma'aikatan jin-ƙai shida a Gaza

Asalin hoton, Reuters
An kashe ƙarin ma'aikatan Majalisar Dinkin Duniya shida a Gaza, a cewar hukumar kula da ƴan gudun hijira ta Falasdinawa UNRWA.
Ya kawo adadin ma'aikatan UNRWA da aka kashe a Gaza tun lokacin da aka fara rikicin zuwa 35.
"Muna jimamin rashin abokan aikinmu yayin da suke yin duk abin da za su iya don taimakawa mabuƙata," Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya wallafa a shafinsa na X a daren Litinin.
- Yaya mamayen ƙasa na sojojin Isra'ila zai kasance a Gaza?
- Rayuwa a Gaza: 'Babu wurin fakewa a ruwan makamai masu linzami'



