Isra'ila ta ce ta tarwatsa maɓuyar 'ƴan ta'adda' a Lebanon

Asalin hoton, Reuters
Kakakin rundunar sojin Isra'ila Daniel Hagari ya bayyana cewa, a cikin sa'o'i 24 da suka wuce, dakarun Isra'ila sun kai hari kan maɓuyar 'ƴan ta'adda' takwas a ƙasar Lebanon.
Bakwai daga ciki an auka musu ne kafin su yi nasarar harba makamai masu linzami da kuma rokoki, in ji shi.
Har ila yau, Hagari ya ce an kai hare-hare kan gungun mayaƙan Hezbollah 20 tun bayan ɓarkewar faɗa a kan iyakar ƙasar a farkon wannan watan.
Yanzu haka dai rundunar ta IDF ta ce ta harba makami mai linzami kan wani abu da ba ta yarda da shi ba da ya shiga sararin samaniyar Isra'ila daga Lebanon.
- Ana kwashe 'yan Isra'ila a ƙauyukan iyaka da Lebanon saboda barazanar hari
- Ko sauran ƙasashe za su iya shiga yaƙin Gaza da Isra'ila?





