MDD ta buƙaci a bar motocin agaji su shiga Gaza yau Lahadi

Asalin hoton, Getty Images
Shugaban Hukumar Agaji ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce yana fatan za a ƙyale motocin kayan agaji kashi na biyu shiga Gaza a yau Lahadi.
Martin Griffiths, ya ce an cimma yarjejeniya da Masar kan ƙyale manyan motocin kayan agaji tsallakawa ta iyakar Rafah.
A jiya Asabar manyan motoci 20 ɗauke da magunguna da abinci suka wuce ta mashigar.
Mista Griffiths, ya yi kiran da a sanya man fetur a cikin kayan da za a kai Gaza.
Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya sun bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin mai tayar da hankali, sannan sun ci gaba da nanata kiran a tsagaita wuta.
