Biden ya goyi bayan bayanin Isra'ila kan mummunan harin asibiti a Gaza, Daga Gareth Evans

Asalin hoton, Reuters
Shugaban Amurka Joe Biden ya ce mummunar fashewar wani abu a asibitin Gaza, ga alama aikin Falasdinawa 'yan ta-da-kayar-baya ne, inda ya goyi bayan bahasin Isra'ila game da aukuwar lamarin, daidai lokacin da yake ziyara a kasar.
Mista Biden wanda ya sauka a Tel Aviv yau Laraba, ya ce ya yi "matukar takaici da bacin rai" dalilin abin fashewar.
Rundunar sojojin Isra'ila ta ce lamarin ya faru ne sakamakon wata roka da Falasdinawa suka harba amma ta kuskure.
Sai dai jami'an Falasdinawa sun ce wani harin Isra'ila ta sama ne ya fada kan asibitin.
Jami'an lafiya a Gaza sun ce kusan mutum 500 ne suka mutu sanadin abin fashewar, sai dai ba a tabbatar da wani hakikanin adadi na wadanda suka mutu ba.
Tashin abin fashewar a asibitin Al-Ahli Arab da maryacen Talata, ya dusashe ziyarar Joe Biden mai cike da dumbin kasada, lamarin da ya kara janyo tunzuri da haddasa zanga-zanga a fadin yankin.
Ya sauka a birnin Tel Aviv ranar Laraba, inda ya samu kyakkyawar tarba daga Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, kafin shugabannin biyu su gudanar da taron manema labarai na hadin gwiwa.
"Na yi matukar takaici da bacin rai kan fashewar wani abu da aka samu a asibitin Gaza jiya," Mista Biden ya ce.
"Bisa la'akari da abin da na gani, ga alama kamar daya bangaren ne ya haddasa lamarin, ba ku ba" ya fada wa Shugaba Netanyahu. "Sai dai akwai dumbin mutane a can waje da ba su tabbatar ba don haka akwai bukatar mu shawo kan dumbin abubuwa."
Shugaban na Amurka ya jaddada goyon bayansa ga Isra'ila kuma ya yi alla-wadai da kungiyar Hamas ta Falasdinawa 'yan ta-da-kayar-baya, wadda ta kaddamar da wani hari da ba a taba ganin irinsa ba kan Isra'ila daga Gaza a ranar 7 ga watan Oktoba.
Harin dai ya yi sanadin mutuwar mutum 1,400.
Akalla mutum 3,000 ne aka kashe a hare-haren ramuwar gayya da Isra'ila ta kai a Gaza, a cewar jami'an lafiya na Falasdinawa.
Shugaba Joe Biden ya shirya tafiya zuwa Jordan daga Isra'ila don ganawa da Sarki Abdullah da jagoran Falasdinawa Shugaba Mahmoud Abbas da kuma Shugaban Masar Abdul Fattah al-Sisi, amma an soke wannan bangare na ziyarar bayan tashin abin fashewa a asibiti ranar Talata.
Jordan ta soke ganawar kuma ta yi alla-wadai da abin da ta kira "wani babban bala'i kuma mummunan laifin yaki". Fadar White House, a lokaci guda, ta ce an cimma shawarar ne "bisa amincewar juna" kuma Shugaba Biden zai kira Mahmoud Abbas da Shugaba Sisi a lokacin da yake komawa gida Amurka.
Ana sa ran Shugaban Amurka zai gana da majalisar tsare-tsaren yaki ta Isra'ila nan gaba a ranar Laraba.
- Isra'ila da Falasɗinawa na zargin juna da kai hari kan asibitin Gaza
- Rikicin Isra'ila da Gaza: Mene ne asalin sa?
Zai yi "tsauraran tambayoyi" don samun kyakkyawar fahimta kan manufofi da bukatun yakin Isra'ila a Gaza, kamar yadda mai magana da yawun Majalisar Tsaron Kasa ta Amurka, John Kirby ya ce.
"Zai yi tambayoyi masu tsauri amma zai yi tambayoyin ne a matsayinsa na aboki," Kirby ya fada wa manema labarai, ya kara da cewa Amurka za ta jaddada bukatar kai kayan agajin jin kai zuwa Gaza, kuma akwai wajabcin a kaucewa kai hari kan fararen hula.
Mista Biden ya kuma gana da ma'aikatan ba da agajin gaggawa wadanda suka kai dauki bayan harin Hamas da kuma wasu da suka rasa makusantansu ko kuma wadanda ake garkuwa da danginsu, a cewar jami'ai.
Isra'ila ta nemi taimakon kayan aikin sojoji cikin gaggawa na dala biliyan goma daga Amurka bayan harin da Hamas ta kai, CBS News, abokiyar kawancen BBC a Amurka ta ruwaito daga abin da ta kira wasu majiyoyi masu alaka da rokon.
Hukumomi a Gaza, wanda Hamas ke karkashin ikon Hamas sun ce mutum 500 ne suka mutu a fashewar da aka samu a asibiti, wanda wani likita ya kira "kisan kiyashi".




















