Atiku ya nemi haɗin kan Kwankwaso da Obi wajen binciken Tinubu

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Mukhtar Adamu Bawa, A'isha Babangida, Rabiatu Kabir Runka and Haruna Kakangi

  1. Abin da ya sa nake bincike kan takardun karatun Tinubu - Atiku

    ATIKU ABUBAKAR

    Asalin hoton, ATIKU ABUBAKAR

    Bayanan hoto, ATIKU ABUBAKAR

    Lauyan ɗan takarar shugaban ƙasa na jami’iyyar PDP ya ce “Takardar shaidar kammala karatu da shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar wa hukumar zaɓe ta INEC na bogi ne.”

    Lauyan ya faɗi haka ne jim kaɗan bayan ɗan takarar, Atiku Abubakar ya kammala ganawa da manema labaru yau Alhamis a Abuja.

    Lauya Kalu Kalu ya ce takardar kammala karatun digiri da Tinubu ya miƙa wa Inec ba na gaskiya ba ne.

    Fadar shugaban ƙasa dai ta sha musanta wannan zargi.

    Taƙaddama ta ɓarke a Najeriya tsakanin Atiku Abubakar wanda ke ƙalubalantar zaɓen shugaba Tinubu, da kuma ɓangaren na shugaban ƙasa ne tun bayan da Atiku ya nace kan samun takardun karatun shugaba Tinubu daga jami’ar jihar Chicago da ke Amurka.

    Sai dai a cikin makon nan ne jami’ar ta fitar da takardun, inda ta tabbatar da cewa Bola Tinibu ya yi karatu a jami’ar.

    Sai dai bayan yin nazari kan takardun an ci gaba da samun ƙorafe-ƙorafe daga ɓangaren Atiku da jam’iyyar PDP, inda suka nuna shakku kan bayanan da ke ƙunshe a cikin takardun.

    Lauya Kalu ya ce takardun da jami’ar ta fitar sun nuna cewa “Bola Ahmed Tinubu ya haɗa takardar kammala karatu ta bogi tare da miƙa wa Inec.

    “Na biyu, sunan da ke jikin takardar karatun da aka yi amfani da ita domin shiga jami’ar jihar Chicago na ƙunshe ne da sunan mace, wanda ke nuna cewa ba na Bola Ahmed Tinubu ba ne.

    “Na uku, Takardar da aka yi amfani da ita wajen shiga jami’ar Chicago ta nuna cewa Bola Ahmed Tinubu ya yi karatunsa na sakandare ne a kwalejin gwamnati da ke Legas, inda ya kammala a 1970, to amma a zahiri an kafa kwalejin ce a 1974.

    “Takardun sun nuna cewa wanda ya mallaki takardar baƙar fata ne ɗan Amurka, amma takardun da Bola Ahmed Tinubu ya gabatar wa Inec ya bayyana cewa ƙasa ɗaya ce kawai yake amsawa, wanda hakan ke nufin cewa ba takardunsa ba ne.

    Bayanan bidiyo, Abin da ya sa nake bincike kan takardun karatun Tinubu - Atiku
  2. An kama mahaifiyar yarinyar da ake zargin ƴan hisbar Iran sun azabtar

    .

    Asalin hoton, EPA

    Wata kungiyar kare hakkin Kurdawa 'yan Iran, ta ce hukumomin kasar sun kama mahaifiyar matashiyar nan da akai zargin 'yan Hizba sun azabtar da ita saboda bata yafa gyalen da ya rufe mata gashi ba.

    Mahaifan Armita Geravand mai shekara 16, sun ce azabar da aka gana mata ta sanya ta shiga mummunann yanayi.

    Wakilin BBC ya ce " ƴan uwan Armita sun ce ta shiga halin rai kwa-kwai mutu kwa-kwai na kwanaki, a ranar Lahadi lamarin ya faru lokacin da Armita ke cikin jirgin kasa tare da kawayenta, gashinta a bude, jami'an Hizba suka fincikota.

    Amma kungiyar kare hakkin ƙurdawan ta ce an tilasta wa mahaifiyar Armita fadin hawan jini ne ya kada 'yar ta.

  3. Za mu gayyato hafsoshin tsaro domin jin matsalolinsu - Sanata Yar'adua

    .

    Asalin hoton, Sen Abdul'aziz Musa Ƴar'adua

    Majalisar dattawan Najeriya ta nuna damuwa game da matslar da ke ci gaba da ƙaruwa ta satar dalibai a jami`o`in kasar.

    Ko a jiya ma `yan bindiga sun sace dalibai mata su biyar a jami`ar Tarayya da ke Dutsin-Ma a jihar Katsina.

    Wannan ne ya sa `yan majalisar dattawan suka yanke shawarar ganawa da hafsoshin tsaron kasar domin duba irin matakan da za a dauka da nufin magance matsalar.

    Sanata Abdul`aziz Musa Yar'adua shi ne ya gabatar da ƙudurin, ya kuma ce " za mu gayyato hafsoshin tsaro domin jin matsalolinsu don a magance su."

    "Satar Jama'a ta fara zama ruwan dare a yankin Arewa,ya kamata gamnati ta tashi tsaye wajen tsare al'umma," in ji Yar'adua.

    "Muna son shugaban ƴan sanda ya aiwatar da tsarin da ya ce zai samar na bayar da tsaro ga ɗalibai da malamansu," cewar Sanata Yar'adua.

    Bayanan sautiLatsa hoton da ke sama don sauraron bayanin da Sanata Abdul'aziz Musa Yar'adua ya yi wa BBC.
  4. Kisan gillar budurwar da aka sace a Zaria ya ɗimauta al'umma

  5. Turkiyya ta janye daga neman shirya gasar Euro 2028

  6. Zan tabbatar an samar da tsaro a jami'ar Gusau - Dauda

    ...

    Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ce hukumomi na bakin kokarinsu wajen ganin sun ceto sauran ɗalibai da ƴan bindiga suka sace daga jami'ar tarayya ta Gusau.

    Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, sa'ilin da ya kai ziyara a harabar jami'ar da ke Gusau.

    A lokacin ziyarar, gwamnan ya kuma sha alwashin ganin an samar da tsaro yadda ya kamata domin a ci gaba da tafiyar da lamurra yadda suka kamata.

    Kusan mako biyu ke nan bayan da wasu ƴan bindiga suka kai hari a unguwar Sabon Gida da ke maƙwaftaka da jami'ar, inda suka yi awon-gaba da ɗalibai sama da 20.

    Daga baya hukumomi sun tabbatar da cewa an samu nasarar karɓo ɗalibai 14 da wasu ma'aikata biyu.

    Sai dai har yanzu sauarn mutanen na a hannun ƴan bidiga.

  7. Hukumomi sun kasa gano silar baƙuwar cutar da ke addabar ɗalibai a Kenya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Binciken da gwamnatin Kenya ta ƙaddamar ya kasa gano mene ne silar wata baƙuwar cuta da ta kama sama da ɗalibai 100 a wata makarantar sakandare da ke yammacin ƙasar.

    Ministar lafiya ta ƙasar, Susan Nakhumicha ta shaida wa manema labaru cewar ɗalibar farko da ta kamu da cutar wata ce da ta je yi tafiya zuwa Nairobi babban birnin ƙasar.

    Binciken ya kasa gano wata ƙwayar cutar 'bacteria' ko 'virus' da za a ce ita ce ta haddasa cutar.

    Ana sa ran ministan ilimi na ƙasar zai yi bayani ga iyaye waɗanda suka damu da halin da yaransu suka faɗa ciki.

    Duk da cewa ba a kulle makarantar ba amma an ƙyale ɗalibai kimanin 1000 su tafi gida.

  8. Makamin Rasha ya kashe mutum 50 a Ukraine

    ..

    Asalin hoton, Presidential office

    Ukraine ta ce harin da Rasha ta kai kan wani ƙauye da ke gabashin ƙasar ya kashe a aƙalla mutum 50.

    Wannan ne harin makami mai linzami mafi muni da Rasha ta ƙaddamar a Ukraine cikin watanni.

    Mahukunta sun ce makamin ya faɗa ne kan wani kanti a ƙauyen Hroza, wanda bai da nisa da birnin Kupyansk.

    Lamarin ya faru ne a lokacin da mutane suka taru domin alhinin mutuwa.

    Cikin waɗanda suka mutu har da wani yaro ɗan shekarta shida.

    Wani bidiyo da aka saki ya nuna yadda hayaƙi ya turnuƙe yankin da abin ya faru, sai kuma ɓaraguzai da gawarwaki.

    Ana ci gaba da gwabza yaƙi tsakanin Rasha da Ukraine, yayin da Rasha ke ƙoƙarin sake karɓe wuraren da Ukraine ta karɓe a bara.

  9. Atiku ya buƙaci Kwankwaso da Peter Obi su haɗa hannu da shi wajen binciken Tinubu

    ...

    Asalin hoton, facebook/Atiku Abubakar

    Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaɓen Najeriya na 2023, Atiku Abubakar, ya bukaci sauran ƴan takara na hamayya, Peter Obi da Rabi’u Musa Kwankwaso su haɗa ƙarfi da shi a ƙoƙarinsa na bincike kan takardun karatun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

    Atiku ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja a yau ranar Alhamis.

    Ya ce abin da yake fafutuka a kai shi ne tabbatar da bin diddigi domin yin adalci da kuma gaskiya a Najeriya.

    Atiku dai ya shigar da ƙara kan shugaban kasa Bola Tinubu game da takardunsa na karatu a jami’ar jihar Chicago.

    Ya bukaci samun takardun ne domin su zama shaida ga zarginsa na jabun satifiket din Tinubu na CSU.

  10. Rashin Messi ya jefa Inter Miami a tsaka mai wuya

  11. Kudin samun izinin sayen mota a Singapore ya kai kimanin naira miliyan 80

    Vehicles

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Singapore street

    Kudin yin takardar izinin mallakar katuwar motar iyali a Singapore ya yi tashin gwauron zabi zuwa wani sabon farashi da bai taba kai wa ba a tarihi.

    A yanzu ana yin takardun izinin mallakar motar ne a kan kudin Singapore dala 146,002 fiye da naira miliyan 80 a canjin hukuma.

    Kasar ta bullo da tsarin mallakar takardar samun izinin sayen mota ta tsawon shekara goma ne wato certificate of entitlement (COE) a 1990, a matsayin wata hanya ta rage cunkoson ababen hawa a kan tituna.

    Mai sha'awar mallakar mota a Singapore jazaman ne sai ya samu takardar izini kafin ya iya sayen wani abin hawa.

    Ana sayar da su ne a wani tsari irin na gwanjo a duk mako biyu, inda gwamnati take iyakance adadin takardun izinin da za a sayar.

    Idan aka hada da haraje-haraje da kudin fito, tsarin ya sa Singapore ta zama kasa mafi tsada ga masu son sayen mota.

    Ga misali, kudin sabuwar dankareriyar mota Toyota kirar Camry Hybrid ya kai kimanin dalar Singapore 250,000, wanda ya hadar da kudin takardar izinin mallakar mota da haraje-haraje. Kudin ya ninka har kusan sau shida ga irin wannan mota a Amurka.

    Akwai takardun izinin mallakar ababen hawa ga masu sayen sha'awar kananan motoci da babura da kuma ababen hawan fasinja.

    Kudin takardun izinin mallakar abin hawa ya kai tsadar da bai taba yi ba a tsawon watanni masu yawa a jere yayin da kokarin farfadowar kasar daga annobar korona ya janyo karuwar bukatun neman izinin da kuma kafin shirin gwamnati na rage kudaden rangwame da gwamnati ke yi ga masu neman izinin a shekara mai zuwa.

  12. An iyakance yawan ƙwan da mutum zai iya saya a Afrika ta Kudu

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Manyan kantunan Afirka ta Kudu na iyakance yawan ƙwan da mutanen ƙasar za su iya saya a lokacin da ƙasar ke fama da ƙarancin kaji saboda barkewar cutar murar tsuntsaye.

    Wasu manyan kantunan sun kayyade adadin ƙwai da abokan ciniki za su iya saya zuwa shida kawai, in ji kafofin watsa labarai na cikin gida.

    Masu kiwon kaji sun yi gargadi a kan karancin kwai da kaji saboda barkewar cutar, da kuma tasirin da katse wutar lantarki ke yi ga harkar kiwo.

    Ma’aikatar noma a makon jiya ta ce an kashe kaji sama da miliyan 2.5, inda cutar ta bazu a larduna biyar daga cikin takwas na Afirka ta Kudu.

  13. Shugaban mulkin sojan Burkina Faso ya kori shugaban rundunar jandarmomi

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, ...

    Shugaban mulkin soja na Burkina Faso ya maye gurbin shugaban 'yan sandan kasar, sama da mako guda bayan gwamnatin kasar ta ce ta dakile yunkurin juyin mulki.

    A ranar Laraba ne, Ibrahim Traoré ya nada Laftanar Kanal Kouagri Natama a madadin Laftanar Kanal Evrard Somda, wanda ya jagoranci rundunar Jandarma tun bara.

    Traoré ya kuma canza jami'an da aka dora wa alhakin kula da kayan aikin rundunar sojojin Burkina Faso da ta jandarma.

    A makon jiya ne, gwamnatin mulkin sojan Burkina Faso ta kama jami’an rundunar jandarma hudu bisa zargin cewa sun kulla wani shirin yi wa ƙasa zagon ƙasa.

    A cewar jaridar Jeune Afrique ta Faransa, biyu daga cikin hafsoshin da aka tsare suna aiki ne a karkashin rundunar Jandarma ta kasa kuma makusantan Kalan Evrard Somda ne.

    A baya dai wanda ya maye gurbin nasa ya jagoranci rundunar jandarma a yankin arewacin Kaya, inda sashen Traore yake.

  14. Mauritius ta soke dokar hana luwadi da madigo

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, ...

    Mauritius ta soke dokar haramta auren jinsi ɗaya a ƙasar

    A ranar Laraba, Kotun Kolin kasar ta bayyana cewa sashe na 250 na kundin laifuffuka na Mauritius, wanda ya fara a shekarar 1898, ya saɓawa kundin tsarin mulkin kasar.

    A karkashin dokar dai, mutanen da aka samu da laifin luwaɗi ko auren jinsi daya na fuskantar barazanar dauri har na tsawon shekaru biyar.

    A hukuncin da ta yanke, Kotun Kolin ta bayyana cewa dokar da aka soke ba ta "nuna duk wata dabi'a ta Mauritius ba amma an gaji ta a matsayin wani bangare na tarihin mulkin mallaka daga Burtaniya".

    Matakin soke dokar hana luwadi da madigo ya zo ne a lokacin da wasu matasan Mauritius hudu daga kungiyar kare hakkin ƴan luwaɗi da maɗigo suka shigar da kara a gaban kotu kan dokar hana luwadi saboda "cin zarafinsu da 'yancinsu" a watan Oktoban 2019.

    Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin kare hakkin bil adama da dama sun yaba da hukuncin.

    Da wannan hukunci, Mauritius ta shiga cikin jerin kasashe masu tasowa na Afirka waɗanda ko dai suka haramta ko kuma suka halatta auren jinsi daya ciki har da Angola da Botswana da Seychelles da kuma Mozambique.

  15. Kotun soja a Najeriya ta samu wani janar da laifin sace miliyoyin nairori

    Army logo

    Asalin hoton, Nigerian Army/Facebook

    Wata kotun soja ta musamman a Najeriya ta sanya ranar 10 ga watan Oktoba don yanke hukunci kan shari’ar da ta yi wa wani babban hafsan soja mai mukamin manjo janar bisa tuhume-tuhumen sata da yin jabun takardu da almubazzaranci da kuma shirya maƙarƙashiya.

    Manjo janar Umaru Muhammed, tsohon Manajan Darakta na kamfanin kula da kadarorin rundunar sojojin kasa ta Najeriya wato Nigerian Army Properties Limited ya gurfana a gaban kotun ne a kan tuhume-tuhume guda 18.

    Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwati shugaban kotun, Manjo Janar James Myam, na cewa wanda ake tuhumar a ranar Laraba, ya ƙi amsa laifi a kan kararrakin da aka gabatar a kansa, inda ya gabatar da shaida biyu a kotu.

    Ya ce a daya bangaren kuma mai kara wato rundunar sojin kasa ta Najeriya ta gabatar da shaida 24 a tsawon shari'ar da aka yi.

    Janar James Myam ya ce tuhuma ta ɗaya an shigar da ita ne a ƙarƙashin sashe na 383, karamin sashe na kundin dokar manyan laifuka na Najeriya.

    Myam ya kara da cewa, an kuma gabatar da tuhumar ne bisa sashe na 114 na dokar Sojoji Cap A20 2004.

    Kotun ta ce ta samu hafsan da ake kara da laifin satar dalar Amurka miliyan 1.04 tsakanin 7 ga watan Mayun 2019, zuwa 24 ga watan Yunin 2021, lokacin da yake aiki a matsayin manajan daraktan kamfanin NAPL.

    Babban alkalin kotun ya kuma ce an samu wanda ake tuhuma - da laifin bai wa wani, Manjo Usman da wani mutum wanda a halin yanzu ake neman su - umarni su dinga karbar kudi da dalar Amurka daga hannun masu jiragen ƙasa.

    Sai dai Janar Myam ya ce ba a samu Janar Umaru Muhammed da laifi ba a tuhuma ta 7, wadda ta kunshi laifin hada baki don yin jabun takardu tare da wani Yusuf Abdulahi.

    Haka zalika shugaban kotun ya ce an kuma samu Janar Umaru Mohammed da laifin yin jabun takardu mai alaka da tuhuma ta 8 da ta 9 a kan satar dala 430,000.

    Kotun ta kuma samu wanda aka yi karar da laifin shirya makarkashiya don yin jabun takardu da sayar da kadarar kamfanin rundunar sojojin kasa a kan naira miliyan 200.

    Sannan ta same shi da laifin daukar kudi naira miliyan 74 cikin wata hanya ta rashin gaskiya daga asusun kamfanin a ranar 22 ga watan Agustan 2019.

    Game da tuhuma ta 14 da 15 da 16 da kuma ta 18, wadanda suka danganci babban laifin yin sama da fadi, kotun ta ce wanda aka yi zargin bai iya yin bayani a kan dukiyar da ta kai naira biliyan 2 da rabi mallakar kamfanin soja ba.

    • 'Muna bincike kan zargin rashin bai wa sojojinmu isasshen abinci'
    • Mun raba Najeriya da ƴan ta'adda fiye da 800 a wata uku - Sojoji
  16. Jami'ar Abuja ta sanya gwajin shan ƙwaya a matsayin sharaɗin ba da damar karatu

    Shugaban Jami’ar Abuja, Farfesa Abdul-Rasheed Na”Allah, ya ce dole ne dalibai masu neman gurbin karatu a jami’ar, su gudanar da gwajin shan ƙwaya a matsayin sharaɗi, kafin samun gurbin karatu.

    Farfesan ya bayyana haka a wajen taron gabatar da jawabi kafin bikin yaye dalibai da suka kammala karatu karo na 27 a ranar Laraba.

    Ya ƙara da cewa jami'ar na aiki da hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya, NDLEA domin taimaka wa daliban da ke shan miyagun kwayoyi da nufin sauya musu hali.

    A cewarsa, sanin matsayin mutum game da tu'ammali da kwaya, abu ne mai muhimmanci da nufin taimaka musu rabuwa da matsalar shaye-shaye.

    Farfesa Abdul-Rasheed Na'Allah ya kuma bayyana cewa dalibai 7,128 ne za su kammala karatu a Jami'ar Abuja bana yayin bikin da za a gudanar ranar Asabar, 7 ga watan Oktoba.

    • Me ya sa jami'o'in Najeriya suka tsuga kuɗin makaranta?
    • Hukumomin Najeriya sun kama bama-bamai 399 da miyagun ƙwayoyi
  17. Rishi Sunak ya kare shirinsa na hana shan taba ga matasa masu tasowa

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Firaministan Burtaniya, Rishi Sunak ya ce shirye-shiryen kawar da siyar da sigari a Ingila zai kasance "babbar sa baki kan lafiyar jama'a a cikin tsararrakin ƙasar.

    Shirinsa ya haɗa da neman a ƙara yawan shekarun shan taba a kowace shekara da shekara guda ta yadda a karshe babu wanda zai iya siyan taba.

    Za a ba wa 'yan majalisar Tory damar kada kuri'a kyauta kan wannan lamari yayin da kuma Labour ta nuna cewa za ta goyi bayan manufofinsa.

    Sai dai wasu masu sukar manufofin sun ce hakan na iya haifar da samar da “kasuwan bayan fage”.

    A bara, masana'antar taba ta tara sama da euro biliyan 10 a haraji, raguwar kashi 3 cikin ɗari daga shekarar 2021 zuwa 2022.

    Da yake sanar da hakan a cikin babban jawabinsa a taron jam'iyyar Conservative, Sunak ya ce ya yi imanin cewa matakin ya dace idan ana son magance matsalar rashin lafiya da za a iya kiyaye wa.

    Sunak ya ƙara da cewa shan taba sigari ba daidai ba ce da cin dankali ko biredi saboda ba zai iya kasancewa cikin mai gina jiki ba, kuma babu wani matakin da ya dace na shan taba.

    • Ranar yaki da shan taba: Abin da ya sa dole masu zama da mashaya sigari su damu da lafiyarsu
    • Wanne abu ne ke ingiza mutane su yi wa kansu lahani?
  18. Faransa ta tsaida ranar fara janye dakarunta daga Nijar

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Dakarun Faransa za su fara janyewa daga Nijar “a wannan makon”, in ji gwamnatin Paris a ranar Alhamis, bayan sun samu saɓani da gwamnatin mulkin soja tun bayan juyin mulkin watan Yuli.

    Hedkwatar sojojin Faransa ta ce "Za mu fara aikin janye dakarun a wannan makon, cikin tsari mai kyau, cikin aminci da hadin gwiwa da Nijar."

    Sanarwar ta zo ne mako guda bayan da jakadan Faransa a Yamai, ya koma gida sakamakon matsin lamba daga gwamnatin kasar.

    Shugaba Emmanuel Macron a ranar 24 ga watan Satumba dai ya ba da sanarwar janye sojojin Faransa 1,400" a karshen shekara.

    Sojojin Faransa sun kasance a Nijar a wani bangare na yaƙi da masu iƙirarin jihadi a fadin yankin Sahel.

    Sojoji Kimanin 400 ne aka tura su aiki tare da sojojin kasar a arewa maso yammacin Nijar, kusa da kan iyaka da Burkina Faso da kuma Mali.

    Yankin mai "iyaka uku", ya yi kaurin suna a matsayin mafaka ga mayaka kungiya masu alaka da Alqaeda da IS.

    Hedkwatar sojojin ta ce dakarun da ke janyewa daga yankin na buƙatar kariya kafin sun bar wuraren da aka jibge su, mai yiwuwa gami da tallafin jiragen sama daga babbar runduna a wani sansanin jiragen sama da ke wajen Yamai, babban birnin kasar.

    Sojojin dai na cikin halin rashin tabbas tun lokacin da gwamnatin mulkin sojan Nijar ta fara neman janyewarsu tare da katse hanyoyin samun abinci, baya ga zanga-zangar kin jinin Faransa da kungiyoyin fararen hula suka rika yi a wajen birnin Yamai.

    A yanzu dai sojojin Faransa za su janye ne ko dai ta kudu, hanyar Benin mai takun saka da gwamnatin mulkin sojan Yamai ko kuma ta Chadi daga gabas, wurin da hedkwatar dakarun Faransa da ke aiki a sahel take.

    A yanzu haka, Yamai ta haramta zirga-zirgar jiragen Faransa a sararin samaniyarta.

    • Shin wane tasiri janyewar dakarun Faransa za ta yi ga Nijar?
    • Ƙasashen Yamma masu dakarun sojoji a Nijar
  19. Gajiya ce ta sanya ni faɗuwa a majalisa - Balarabe Abbas Lawal

    ...

    Asalin hoton, KADUNA STATE GOVERNMENT/FACEBOOK

    Ministan shugaban Najeriya Bola Tinubu, Balarabe Abbas Lawal wanda ya yanke jiki ya faɗi lokacin da ake tantance shi ranar Laraba a zauren majalisar dattijai ya ce gajiya ce ta sanya shi faduwa.

    Ministan wanda ya fito daga jihar Kaduna ya faɗi ne bayan ya kammala jawabi game da tarihin rayuwa da karatunsa.

    "Yanzu lafiya lau nake ji, an duba ni a asibiti kuma an ba ni magani, gajiya ce kawai, ba wani abu ba ne,” ministan ya shaida wa manema labarai.

    Ministan wanda majalisa ta tabbatar da shi ya fito ne cikin murmushi amma a fuska ana iya gane yana cikin gajiya.

    Majalisar dattijai dai ta katse zaman tantancewar da take yi bayan faduwar Balarabe Lawal inda ta koma zaman sirri kafin ta tabbatar da shi tare da sauran wadanda Shugaba Tinubu ya aika sunayensu ga majalisar.

    • Manyan ƙalubalan da ke gaban sabbin ministocin tsaron Najeriya
    • Mutanen da suka samu shiga ƙunshin ministocin Tinubu
  20. Rikicin Haiti ba matsalar Kenya ba ce – Odinga

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Jagoran 'yan adawar Kenya Raila Odinga ya nuna shakku kan matakin da kasar ta dauka na jagorantar rundunar tabbatar da zaman lafiya a kasar Haiti domin yaki da tashe-tashen hankula a can, yana mai bayyana matakin da cewa ba daidai ba ne.

    Odinga, a wata hira da ya yi da wani gidan talbijin na kasar ranar Alhamis, ya ce shirin tura ‘yan sandan Kenya zuwa Haiti ba shi ne abin da ya kamata Kenya ta sanya a gaba ba. Ya kara da cewa tuni yankin gabashin Afirka yake fama da nasu “dumbin matsaloli”.

    "Kafin ma ku zo Afirka, Haiti tana bakin kofar Amurka wadda ita ce kasa mafi karfi a duniya. Me ya sa za a dora wa Kenya alhakin jagorantar rundunar kasashen duniya a Haiti?"

    Odinga ya ce halin da ake ciki a Haiti yana da hatsari, inda ya yi gargadin cewa shirin tura jami'an tsaron zai jefa rayukan 'yan sandan Kenya cikin hatsari.

    "Lokacin da akwatunan gawawwaki suka fara isowa nan, a lokacin ne za mu yi nadama. Haiti na da hatsari kuma akwai yiwuwar 'yan sandanmu su fuskanci matsaloli a can," in ji shi.

    "Matsalar Haiti ta siyasa ce, ba wai bindiga take bukata ba, tana bukatar tattaunawa ne." Odinga ya kara da cewa.

    A ranar Litinin ne kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da tura dakarun kasashen duniya na tsawon shekara guda tare da yin nazari kan matsayinsu a kasar bayan wata tara.

    Shugaban Kenya, William Ruto ya yi alkawarin cewa "ba za su bai wa al'ummar Haiti, kunya ba".

    Sai dai kuma wasu masu sukar lamirin matakin sun nuna rashin amincewarsu da shirin, inda suke nuna shakku kan yadda 'yan sandan Kenya za su iya fuskantar gungu-gungun 'yan bindiga a Haiti.

    • Babban birnin da 'yan bindiga ke cin karensu babu babbaka a cikinsa
    • Masu zanga-zanga sun yi wawaso da sa wuta a gonar tsohon shugaban Kenya