'Yan ƙwadago sun sanar da aniyar shiga yajin aiki a Najeriya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Haruna Kakangi and Zulaiha Abubakar

  1. Majalisar Dattijai za ta tantance shugaban CBN da Tinubu ya naɗa

    ...

    Asalin hoton, CITIBANK

    A yau ne Majalisar Dattawa za ta gudanar da aikin tantance Olayemi Cardoso, tsohon Shugaban Bankin Citi a Najeriya a matsayin Gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN.

    Bugu da kari kuma, za a tantance wasu mutane hudu da aka zaɓa a matsayin mataimakan gwamnonin Babban Bankin Najierya, domin su hada karfi da karfe da Cardoso don tafiyar da harkokin bankin a cikin shekaru biyar masu zuwa.

    A cikin wata sanarwa da ofishin yada labarai na shugaban majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele ya fitar, majalisar za ta tantance duk waɗanda aka miƙa sunan su bayan ta dawo daga hutun ta na shekara.

    Sanarwar ta kara da cewa, “Majalisar dattawan tarayyar Najeriya za ta koma zaman ta a ranar Talata 26 ga watan Satumba. Za mu yi nazari kan tantance Dr. Cardoso a kwamitin baki daya.“

    "Za a kuma tantance mataimakan gwamnoni hudu da suka hada da Emem Nnana Usoro da Muhammad Sani Abdullahi Dattijo da Philip Ikeazor da kuma Dakta Bala M. Bello.“

    A ranar 15 ga watan Satumba ne shugaba Tinubu ya amince da nadin Cardoso a matsayin sabon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN).

    Ya kuma amince da nadin mataimakan gwamnoni hudu na tsawon shekaru biyar kowanne a matakin farko, har zuwa lokacin da majalisar dattawan tarayyar Najeriya ta amince da su.

    • Wane ne sabon Gwamnan CBN Olayemi Cardoso?
    • Tinubu ya dakatar da gwamnan CBN Emefiele
  2. Gwamnati ba ta sasantawa da ƴan bindiga - Badaru

    Badaru

    Asalin hoton, Twitter/Ministry of Defence

    Ministan tsaron Najeriya, Muhammad Badaru Abubakar ya musanta zargin da gwamnan jihar Zamfara ya yi na cewa gwamnatin tarayya na ƙoƙarin sasantawa da ƴan bindiga.

    A wata sanarwa da aka wallafa a shafin X na ma'aikatar tsaron Najeriya, ministan ya ce gwamnatin tarayya ba ta umurci wani ko wasu su tattauna da ƴan bindiga a madadinta ba.

    Sanarwar ta kara da cewa gwamnatin Tinubu na aiki domin ceto sauran daliban Jami'ar Tarayya da ke Gusau, waɗanda aka sace a ranar Juma'a.

    A cewar Badaru a yanzu haka sojoji sun ceto dalibai 13 da kuma leburori uku daga cikin mutanen da ƴan bindiga ke garkuwa da su.

    A ranar Litinin ne gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya fitar da wata sanarwa inda ya zargi Gwamnatin Tarayya da yin tattaunawar sirri da ƴan fashin daji a jihar Zamfara ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

    Sai dai da yammacin Litinin, wata sanarwa daga ofishin ministan yaɗa labaru da wayar da kan al'umma na Najeriya ta musanta batun, tare da zargin gwamnan na jihar Zamfara da ƙoƙarin siyasantar da batun tsaro.

    Sai dai duk da haka gwamnan, ta hannun mai taimaka masa kan yaɗa labaru da hulɗa da jama'a ya sake fitar da wata sanarwar a ranar Talata inda ya ce gwamnatin jihar tana da shaidu na irin tattaunawar da ta gudana tsakanin jami'an gwamnatin tarayya da ƴan fashin dajin.

    Masana tsaro na kallon musayar kalaman tsakanin ɓangarorin biyu a matsayin wani abu da ka iya yin cikas ga ƙoƙarin gwamnati na yaƙi da ayyukan ƴan fashin dajin a yankin na arewa maso yammacin Najeriya.

    • 'Rashin haɗin kan gwamnatoci dama ce ga 'yan bindiga'
    • An ceto sama da mutum 60 daga ƴan bindiga a jihar Zamfara
  3. Ƙungiyar ƙwadago za ta yanke shawara kan shiga yajin aiki

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyar Kwadago ta Najeriya za ta gudanar da wani taron gaggawa na majalisar zartarwa ta kasa game da shirin da take yi na shiga yajin aikin sai baba ta gani.

    Wannan matakin ya biyo bayan cikar wa'adin kwanaki 21 da ƙungiyar ta bai wa gwamnati don biya musu buƙatu.

    A cikin wata takardar gayyata da ta tura wa manema labaru a yau Talata, NLC ta ce za ta gana da manema labarun a ranar ta yau domin tabbatar masu da matsayar da ta cimma.

    Ƙungiyar dai a baya ta shirya yajin aikin gama-gari da ta gudanar a ranakun 5 da 6 ga watan Satumba, saboda tsadar rayuwar da ƙasar ta shiga sakamakon cire tallafin man da shugaba Bola Tinubu ya yi.

    Bugu da kari, kimanin wata guda da ya gabata, ƙungiyar ƙwadagon sun shiga yajin aikin don magance irin matsalolin da suka shafi tsadar rayuwa, sai dai daga bisani suka dakatar da yajin aikin bayan tattaunawa da shugaba Bola Tinubu.

    • Ko yaya yajin aikin ƙungiyar ƙwadago ya kasance a jihohin Najeriya?
    • Kalaman 'yan Najeriya bayan sake ƙara kuɗin man fetur
  4. Jikar Nelson Mandela ta rasu

    ...

    Zoleka Mandela, jikar zababben shugaban kasar Afirka ta Kudu na farko ƙarƙashin dimokuradiyya, Nelson Mandela, ta rasu tana da shekaru 43 sakamakon kamuwa da cutar daji.

    Iyalanta sun sanar da rasuwar ta a shafin Instagram, inda suka bayyana cewa ‘yan uwa da abokan arziƙi da dama sun kewaye gawar tata.

    A cikin 'yan shekarun nan ta shahara wajen bayar da bayani game da cutar dajin da take fama da ita da kuma bayyana tarihinta na ɗabi'ar shan ƙwayoyi da tsananin damuwar da take shiga da kuma yadda aka yi lalata da ita tun tana ƙarama.

    Zoleka ta kuma yi kamfe don samar da ingantaccen tsaro a kan titi bayan mutuwar diyarta mai shekaru 13 a wani hatsarin mota a shekarar 2010. Zoleka ta rubuta tarihin rayuwarta, wanda ta yi wa laƙabi da 'when hope whispers'.

    Ta kuma yi fama da cutar kansar nono sama da shekaru goma da suka wuce.

    A shekarar da ta gabata ne ta tabbatar da cewa tana da cutar daji a hanta da huhu, daga nan kuma ta yadu zuwa wasu sassan jikinta.

  5. Gobara ta kashe ƴan gudun hijira a Nagorno-Karabakh

    reauters

    Asalin hoton, Reuters

    Mahukunta a Armeniya sun bayyana cewar kusan mutane 300 na kwance a asibiti yayin da gommai ke cikin mawuyacin hali sakamakon ƙonewa lokacin da wani abu ya fashe a wurin ajiye mai.

    Ibtila'in ya faru a lokacin da gwamnatin Armeniya ta bayyana adadin ƴan gudun hijirar da yawansu ya kai 13,350 ne suka shiga ƙasar daga yankunan daban-daban.

    Kusan al'ummar Armeniya 120,000 ne ke zaune a Nagarno-Karabakh yankin da ya ke fuskantar tashin hankali.

    Babu tabbacin abin da ya haifar da fashewar da yammacin Litinin a birnin Stepanakert, amma Ƙungiyar Kare Haƙƙin Ƴan Adam ta Gegham Stepanyan ta walafa a shafinta na sada zumunta cewar sama da mutane 200 sun samu mananan raunuka.

    • Armenia- Azerbaijan: Mutun 100 sun mutu kan Nagorno-Karabakh
    • Armenia-Azerbaijan: Mene ne musabbain rikicin Armenia da Azerbaijan?
  6. Muna da hujjojin cewa Gwamnatin Tarayya na tattaunawar sirri da ƴan fashi - Dauda

    ...

    Asalin hoton, DAUDA LAWAL/INSTAGRAM

    Bayanan hoto, ...

    Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa na da isassun bayanai da ke tabbatar da cewa akwai wasu jami'an Gwamnatin Tarayya da ke jagorantar tattaunawar sirri da ƴan fashin daji a jihar.

    Gwamnan ya faɗi hakan ne a wani martani da ya mayar wa Gwamnatin Tarayya, a yau Talata, bayan wata sanarwa da gwamnatin ta fitar a ranar Litinin tana ƙalubalantar gwamnan game da zargin da ya yi na cewa Gwamnatin Tarayya na tattaunawa da ƴan bindiga a jihar.

    Sanarwar da ta fito daga ministan yaɗa labaru da wayar da kan al'umma na Najeriya, ta zargi gwamnan na Zamfara da sanya siyasa cikin harkar tsaro.

    Sai dai a martanin da ya mayar ta hannun mai ba shi shawara kan yaɗa labaru, Bala Idris, gwamnan na Zamfara ya ce "muna da sahihan bayanai da shaidu game da abin da ya faru tsakanin wakilan gwamnatin tarayya da ƴan fashin daji a lokacin jerin tattaunawar da aka yi a wurare daban-daban a jihar Zamfara."

    Amma sanarwar ta ce gwamnatin Zamfara ba ta da niyyar fallasa sunayen wakilan Gwamnatin Tarayyar da suka yi tattaunawar a kafafen yaɗa labaru saboda girmama hukuma da kuma tsarin doka.

    Haka nan gwamnatin jihar ta soki lamirin ministan yaɗa labarun na Najeriya kan martanin da ya mayar mata a ranar Litinin, inda ta ce ya yi hakan ne ba tare da yin binciken da ya dace ba.

    Ita dai gwamnatin Zamfara ta ce an gudanar da tattaunawar da ta yi magana a kai ne a yankunan Birnin Magji da Maradun da Mun Haye da Ajah da Bawo da kuma Bagege.

    A martanin na ranar Talata, gwamnatin Zamfara ta ce "Tattaunawa da ƴan bindiga babban kuskure ne wanda ba za ta so ta aikata ba, kuma hakan ba zai kawo ƙarshen matsalar ba, face ma, ya ƙara ƙarfafa wa ƴan fashin gwiwa."

    A ranar Litinin ne dai Gwamnatin Tarayya a cikin sanarwar da ta fitar ta ce "Babu wani jami'in gwamnatin Tarayya da ke tattaunawa da wani ɗan bindiga ko ƙungiyar ƴan bindiga."

    "Sai dai gwamnatin a shirye take ta yi amfani da duk wata hanya wajen sassauta yanayi na tashin hankali da ake ciki da kuma mayar da zaman lafiya a yankunan da ƴan fashin daji suka addaba."

    Zamfara dai na a sahun gaba cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da matsalar rashin tsaro ta ƴan fashin daji ke ci gaba da yi wa illa.

    Ko a makon da ya gabata, ƴan daji sun kai hari a gidajen kwanan ɗaliban Jami'ar Tarayya da ke Gusau, inda suka yi awon-gaba da ɗalibai da dama, waɗanda har yanzu wasu daga cikin su ke hannun ƴan fashin.

    • 'Babu mu babu Sulhu da 'yan fashi a Zamfara'
    • 'Rashin haɗin kan gwamnatoci dama ce ga 'yan bindiga'
  7. Rasha ta sake miƙa buƙatar shiga kwamitin kare hakkin bil adama na MDD

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Rasha na neman sake zama mamba, a kwamitin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya, bayan dakatar da ita sakamakon mamayar Ukraine a bara.

    BBC ta samu kwafin takardar da kasar ta aika wa mambobin Majalisar Dinkin Duniya, inda a ciki take gabatar da wasu matakai da ta kira na magance matsalolin take hakkin dan adam a duniya.

    Wannan dai na faruwa ne duk da wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya a ranar litinin ya bayyana laifukan yaki da Rasha ke aikatawa kan fararen hula a Ukraine, kamar azabtarwa da fyade.

    Jami'an diflomasiyya sun yi iƙirarin cewa Rashar na bai wa ƙasashe makamai da hatsi don samun kuri'unsu. Za ta fafata da Albaniya da Bulgaria wajen neman kujara a kwamitin a zaben da za a yi a watan gobe.

    • Shin juyin mulki Wagner ke yunƙurin yi wa Putin?
    • Me ya sa Amurka ta damu da ƙawancen Putin da Kim Jong Un
  8. Koriya ta Kudu ta jagoranci taro da jakadun Japan da China

    Koriya ta Kudu na gudanar da wani taro da ba kasafai ake yin sa ba tsakanin manyan jami'an diflomasiyyarta da takwarorinsu na Japan da China.

    Ana kallon tattaunawar da kasashen uku ke yi a matsayin wani yunƙuri na ɗan yayyafawa Beijing ruwa a kan damuwarta game da kawancen tsaro da Tokyo da Seoul ke karfafawa da Washington.

    Ma'aikatar harkokin wajen Koriya ta Kudu ta ce taron zai kuma yi duba a kan yiwuwar dawo da taro tsakanin shugabannin kasashen uku.

    • Yadda matasa a Koriya Ta Kudu ke ado da takunkumi duk da wucewar Korona
    • Muhimman abubuwa da za ku so sani game da Koriya ta Arewa
    .

    Asalin hoton, REUTERS/KCNA

  9. Guguwa ta lalata hanyoyi da gidaje a Afrika ta kudu

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, ...

    Hukumomin Afirka ta Kudu na neman mutanen da suka bata tare da tantance barnar da aka yi a lardin Western Cape bayan wata mummunar guguwa da ta afka wa yankin a karshen mako.

    Ambaliyar ruwa ta yi barna sosai ciki har da lalata gidaje, lamarin da ya tilastawa wasu ficewa.

    Hakanan guguwar ta lalata tituna da gadoji da sauran ababen more rayuwa da kuma wasu wuraren da ba za a iya shiga ba tare da la'akarin hanyoyi da dama da ba su da tsaro.

    Hukumomin birnin Cape Town sun ce kungiyoyi suna samun ci gaba wajen maido da katsewar wutar lantarki da ke da alaka da guguwa a yankuna da dama.

    Sai dai ya kara da cewa ba a iya bayyana lokacin da za a kammala gyaran ba saboda yanayin da kuma girman barnar da guguwar ta yi.

    • Mahaukaciyar guguwa da ta shafe fiye da wata ɗaya tana ɓarna
    • Guguwa mai karfi ta jefa mutane cikin duhu a Amurka da Canada
  10. Assalamu Alaikum

    Masu bibiyar wannan shafi barkan mu da safiyar Talata

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye tare da ni Aisha Babangida da Zulaiha Abubakar

    Ku kasance da mu domin sanin irin wainar da ake toyawa a faɗin duniya, musamman ma a Najeriya da makwabtanta