Ba mu da niyyar ruguza Nijar - Ecowas

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza and Haruna Kakangi

  1. Yaƙin Sudan na neman ruguza ƙasar - MDD

    s

    Asalin hoton, AFP

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce yaƙin da ake yi a Sudan na neman durkusar da ilahirin ƙasar, tare da jefa ta cikin mummunan bala'i.

    A tsakiyar watan Afrilu ne fada ya ɓarke tsakanin sojojin ƙasar da dakarun RSF.

    MDD ta ce dubban yara ne ke fama da cutar tamowa, waɗanda ke cikin hatsarin mutuwa, sakamakon rashin samun abinci da magunguna.

    Babban jami'in bayar da agaji na Majalisar Dinkin Duniya, Martin Griffiths,ya ce yunwa da cututtuka da kuma barin gidaje da mutane ke yi na barazana wargajewar Sudan.

    Mista Griffiths ya ce matuƙar ba a kawo ƙarshen yaƙin ba, ilahirin ƙasar za ta iya rugujewa.

    Cikin wannan makon ne Gidauniyar 'Save The Children' ta ce yaƙin ya tilasta mata dakatar da ayyukanta a ƙasar.

    Gidauniyar ta ce fiye da ƙananan yara 30,000 ne suka rasa kulawa a ƙasar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar kuan 500.

  2. Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 32 a Nijar

    d

    Asalin hoton, AFP

    Kamfanin dillancin labaran Nijar ANP ya ce ambaliyar ruwa ta kashe mutum 32 cikin watannin baya-bayan nan.

    "Yankin Tahoua da ke kudancin ƙasar ne matsalar ta fi ƙamari, inda mutum 12 suka mutu, sai Maradi mai mutum 10 da Zindir inda mutane shida suka mutu", kamar yadda ANP ya ruwaito daga ma'aikatar cikin gida ta ƙasar.

    Sai Tileberi mai mutum biyu, da kuma Yamai da Diffa masu mutum ɗaiɗai.

    Rahoton ya ce mutum tara daga ciki sun mutu ne, bayan da gidajen da suke ciki suka rufta, yayin da 23 suka mutu sakamakon nutsewa a cikin ruwan.

    Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da ake samu cikin takiyar kowace damina, na haifar da ɓarna mai yawa a ƙasar.

  3. Trump ya zama shugaban Amurka na farko da aka ɗauki hotonsa a gidan yari

  4. Sojojin Najeriya sun binne gawarwakin dakaru 20 da aka kashe a Neja

    as

    Asalin hoton, NAF

    Rundunar sojin Najeriya ta binne gawarwarkin dakarunta 20 da 'yan bindiga suka kashe a wani kwanton-ɓauna da suka yi musu a jihar Neja.

    A makon da ya gabata sojojin suka ce dakarunsu 36 aka kashe a ani kwanton-ɓauna da 'yan ta'adda suka yi musu a kan hanyar Zungeru zuwa Tegina, sannan kuma da faduwar wani jirgin yaƙin sojin a yankin Chukuba da ke ƙaramar hukumar Shiroro a jihar Neja.

    Rahotonni sun ce jana'izar ta samu halartar ministocin tsaron kasar biyu Muhammad Badaru Abubakar da Bello Matawalle, tare da babban hafsan tsaron ƙasar Janar Christopher Musa.

    Sauran manyan baƙin da suka halarci jana'izar sun haɗar da babban hafsan sojin ƙasa Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, da babban hafsan sojin ruwa na ƙasar da sauran iyalan gwarazan dakarun da suka mutu.

  5. Mali, Prigozhin da Wagner - shin me ya rage?

    Prigozhin

    Asalin hoton, Reuters

    Kwanaki kaɗan kafin faɗuwar jirgin saman da aka yi amanna cewa Yevgeny Prigozhin na cikinsa, shugaban na Wagner ya bayyana a wani bidiyo da aka ce an ɗauke shi ne a Afirka, inda wasu rahotonni suka ce a mali ne.

    Ƙasar Mali - wadda ke a yankin yamacin Afirka - na ɗaya daga cikin ƙasashen da Wagner ke shawa'ar zuwa.

    A yayin da shugabannin mulkin sojin Mali ke ƙara ƙarfafa alaƙarsu da Moscow, sun buƙaci dakarun Faransa da na Majalisar Dinkin Duniya su fice daga ƙasar, inda suka nemi taimakon dakarun Wagner

    Akwai sojojin Wagner akalla 1,000 a Mali, ƙasa da yawan dakarun Majalisar Dinkin Duniya da suka fice daga ƙasar.

    To sai dai akwai fargabar cewa dakarun na Wagner ba za su iya kawar matsalar masu iƙirarin jihadi a ƙasar ba, akwai kuma damuwa game da ɗabi'un dakarun Wagner a ƙasar, bayan da Majalisar Dinkin Duniya ta zarge su da haɗa kai da sojojin Mali wajen aikata zalunci.

    Matsalar shugabanci da kamfanin Wagner ke fuskanta ka iya haifar da fargaba kan yadda Mali za ta dogara da kamfanin don magance matsalar tsaron da take fuskanta.

  6. Akwai tabbacin yiwuwar Prigozhin ya mutu - Ma'aikatar tsaron Birtaniya

    g

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar harkokin tsaron Birtaniya ta ce duk da cewa babu wata ƙwaƙƙwarar hujjar da ke nuna cewa shugaban kamfanin sojojin hayar Rasha na Wagner, Yevgeny Prigozhin na cikin jirgin da ya faɗi, ''akwai tabbacin yiwuwar cewa ya mutu''.

    Jami'ai sun ce sun san yadda Prigozhin ya ƙware wajen ɗaukar matakan tsaro", to amma sun yi amanna da binciken Amurka da ke cewa Prigozhin na cikin jirgin da ya faɗi.

    Ma'aikatar tsaron Birtaniyar ta ce akwai yiwuwar kamfanin Wagner ya tarwatse sakamakon matsalar shugabanci da kamfanin ke fuskanta.

    Abin da zai sa Prigozhin ya yi wahalar samun magaji.

  7. Tinubu ya buƙaci a gaggauta warware matsalar da ke tsakanin Najeriya da UAE

    Nigerian Presidency

    Asalin hoton, Nigerian Presidency

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi kiran da a gaggauta kawo ƙarshen rashin jituwar da ke tsakanin ƙasar da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, wanda ya shafi jigilar jirage da bayar da biza takanin ƙasashen biyu.

    Tinubu ya yi kiran ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin jakadan UAE a Najeriya Ambassador, Salem Saeed Al-Shamsi a fadarsa da ke Abuja.

    A shekarar da ta gabata ne UAE ta dakatar da bayar da biza ga 'yan Najeriya bayan da kamfanin jirgin sama na Emirates ya dakatar da jigila a Najeriya saboda hana shi wasu haƙƙoƙinsa, saboda wasu ƙa'idoji na kuɗaɗen ƙasashen waje.

    Kamfanin ya ce ya ɗauki matakin ne bayan duk wani yunƙuri da ya yi na warware matsalar da hukumomin Najeriya ta hanyar lalama ya ci tura.

    Shugaba Tinubu ya ce ya kamata a gaggauta warware matsalar, yana mai cewa a shirye yake ya shiga tsakani da kansa, don kawo ƙarshen matsalar.

    “Mu kalli abin a matsayin saɓani na 'yan uwataka, domin mu warware shi cikin sauki, dole mu yi aiki tare, Muna buƙatar amincewa da dokokin bai daya kan jigilar jiragen sama da batun 'yan ci-rani," in ji Tinubu.

  8. Trump ya miƙa kansa zuwa gidan yari a Amurka

    Trump

    Asalin hoton, FULTON COUNTY SHERIFF'S OFFICE

    Tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya miƙa kansa ga hukumar gidan yari na Fulton a jihar Georgia inda aka ɗauki tambarin yatsu da hotonsa.

    Ya Shaida wa 'yan jarida a wajen gidan kaso da ke jihar Georgia, tuhume-tuhumen da ake masa karya ce tsagwaron ta.

    Ana tuhumar da yunƙurin sauya sakamakon zaɓen jihar, da ta da zaune-tsaye da tunzura magoya bayansa yin bore a majalisar dokokin Amurka.

    An dai bayar da belinsa kan dala dubu 200. Amma ya barin wurin sai ya wallafa hotonsa da aka dauka a gidan yarin, tare da rubutu a ƙasa "Karka taba miƙa wuya".

  9. Sojojin Nijar sun amince da tura sojojin Mali da Burkina Faso zuwa ƙasar

    m

    Asalin hoton, AFP

    Jagoran juyin mulki a jamhuriyar Nijar, Janaral Abdourahamane Tchiani, ya rattaba hannu kan wata doka da za ta bai wa gwamnatocin soji a ƙasashen Mali da Burkina Faso tura dakaru zuwa ƙasar domin taimakawa wajen tsare ƙasar daga harin ƙungiyar ECOWAS.

    Sanarwar na zuwa ne lokacin da ministocin harkokin wajen Burkina Faso Olivia Rouamba da na Mali Abdoulaye Diop, suka kai ziyara Nijar a jiya Alhamis.

    Kungiyar ECOWAS dai ta yi barazanar afka wa Nijar din domin mayar da ƙasar kan turbar Dimukradiyya ta hanyar amfani da karfin soji.

    ECOWAS ta yi kira ga sojin juyin mulkin su saki shugaba Mohamed Bazoum da mai dakinsa da ɗan shi, da suke tsare da su, tun bayan hambarar da gwamnatinsa, a watan da ya gabata.

  10. Assalamu alaikum

    Masu bin mu a shafinmu na kai-tseye, Abdullahi Bello Diginza ke fatan kun wayi gari lafiya.

    Barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'a, da Hausawa ke yi wa kirari da 'Haji Babbar rana', domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a faɗin duniya, musamman Najeriya da makwabtan ƙasashe.

    Kuna iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.